• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Zazzau Ya Buƙaci Addu’ar Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Sarkin Zazzau Ya Buƙaci Addu’ar Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai martaba Sarkin Zazzau, Mal. Ahmed Nuhu Bamalli, ya yi kira ga al’ummar Nijeriya da su ƙara duƙufa wajen gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya da kwanciyar hankali gami da yin addu’ar neman kawo ƙarshen matsalolin tsaro da suka addabi ƙasar nan.

Sarkin wanda ya yi wannan kiran a yayin bikin baje kolin al’adun gargajiya na shekara-shekara da Masarautar Kaltungo ta jihar Gombe ta saba shiryawa, ya kuma neman ƙarin addu’o’i wa gwamnatoci domin samun nasarar sauƙe nauyin da ke kawukansu wajen shawo kan matsalolin da ake fuskanta a ƙasar nan.

  • Tarihin Katsina Daga Karni Na Goma
  • Cire Tallafin Mai: Magani Mai Daci Ga Kashi 99 Cikin 100 Na ‘Yan Nijeriya

Nuhu Bamalli wanda shi ne uban taron, ya ce, babu wata ƙasa da za ta cigaba ba tare da zaman lafiya da kwanciyar hankali ba, don haka ne ya nemi jama’a da su kauce wa shiga dukkanin wani abun da ka iya janyo matsala ga zaman lafiyar ƙasa.

Ya kuma yaba wa Sarkin Kaltungo, Injiniya Sale Muhammadu Umar da ya kasance mai shirya taron da ke ƙara haɗa kan al’ummar masarautarsa da kuma yadda yake nuna damuwa wajen cigaban al’ummarsa haɗi da kiyaye tarihi da al’adun masarautar.

Sarkin Zazzau

Labarai Masu Nasaba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Shi kuma a nasa jawabin, gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bada tabbacin gwamnatinsa na cigaba da kiyaye rayuka da dukiyar al’ummar jihar tare da bada gagarumin gudunmawa wajen bunqasa al’adun da jihar ke da su.

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Dakta Manasseh Daniel Jatau, ya hori jama’a da a kowani lokaci su kasance masu mutunta sarakuna da al’adun gargajiya domin kyautata cigaba mai ɗaurewa.

Shi kuma a nasa ɓangaren, shugaban taro, Hon. James Joseph Damara (Kauran Kaltungo), ya gode wa irin shugabanci na kwarai da sarkin Kaltungon ke yi wajen kasancewa uba ga kowani ɗan masarautar haɗi da ‘yan uwanta da ke ƙara kyautata zaman lafiya a tsakanin al’ummar masmasarautar.

Ya ce, muhimmancin al’ada baya misaltuwa, yana mai cewa, a bisa mutunta al’ada ne manyan baƙi suka fito daga sassa daban-daban domin halartar wannan taron a Kaltungo, ya misalta sarkin garin a matsayin wani jarumin da ke da buƙarin haɗa kan jama’a da bunqasa al’adu da zaman lafiya a kowani lokaci.

A bikin dai wanda sarkin ya saba gudanarwa, ana baje kolin al’adun gargajiya da raye-raye gargajiya haɗi da baje nau’ikan kalolin abinci da ake da su a masarautar Kaltungo da ma makwafta, inda kowace ƙabila ke fitowa ta nuna asalin al’adarta da ke zama gwanin sha’awa ga mahalarta taro.

Taron wanda ake shafe kusan mako gudana a na gudanarwa, sarkin na kuma shirya taron liyafa na musamman wa ‘yan jarida da sarakuna da sauran manyan baƙi.

Sarkin Zazzau

A wajen liyafar da sarkin ya shirya wa ‘yan jarida, tsohon shugaban ƙungiyar ‘yan jarida na jihar Bauchi, Malam Ibrahim Muhammad Malamgoje, ya yi kira ga masu hannu da shuni ko gwamnati da su kafa wata gidan rediyo ko talabijin a ƙaramar hukumar Kaltungo lura da yadda sarkin ke so da qaunar ‘yan jarida haɗi da mutunta aikin nasu.

A cewar Ibrahim wanda wakilin RFI Hausa ne, a dukkanin yankin arewa babu wani sarkin da ke gayyatar ‘yan jarida daga sassa daban-daban na ƙasar nan kawai domin ya zauna da su ya shirya musu ƙasaitaccen liyafa haɗi da jinjina wa irin qoqarin da suke bayarwa wajen cigaban ƙasa.

A nasa ɓangaren, Sarkin Kaltungo, ya ce, ‘yan jarida na da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen cigaban ƙasar nan, don haka akwai buƙatar a kasance ana jinjina wa irin ƙoƙarinsu a kowani lokaci. Kazalika ya kuma yaba wa irin ƙoƙarin jami’an tsaro su.

Ita kuma jigon taron, Hajiya Sa’adatu Saad Mustapha, ta ce, a kowani shekara ‘yan jarida sun kasance masu tallata irin al’adu da masarautar ke da su, don haka ne ta nuna ‘yan jarida a matsayin abokan jere.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KaltungoMasarautar BauchiZazzau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masarautar Adamawa Ta Naɗa Hakimai 3 A Gundumar Ƙaramar Hukumar Hong

Next Post

Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON – Peseiro

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

29 minutes ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

1 hour ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

3 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

4 hours ago
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
Labarai

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

12 hours ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

17 hours ago
Next Post
Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON – Peseiro

Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON - Peseiro

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

July 5, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

July 5, 2025
Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

July 5, 2025
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

July 5, 2025
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.