• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Fuskantar Koma-baya A Noman Alkama, Masara Da Gero – Rahoto

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya Na Fuskantar Koma-baya A Noman Alkama, Masara Da Gero – Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani rahoton hadaka na hasashen harkokin kasuwanci na yankin Afirka, wanda Hukumar Abinci da Aikin Gona ta Duniya (FAO), tare da shirin samar da abinci na duniya (WFP) suka wallafa a kwanan baya, an yi hasashen cewa, za a samu koma baya a bangaren noman kayan amfanin gona a Nijeriya, Nijar, Chadi da kuma Mali.

A cewar rahoton, an yi hasashen tashin farashin wadannan kayan amfanin gona a daukacin wannan nahiya, a yayin kuma da ake sa ran ci gaba da kara bukatarsu.

  • Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023
  • Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Tantuna Don ‘Yan Gudun Hijira Da Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kazalika, rahoton ya danganta afkuwar hakan a kan kalubalen hada-hadar kasuwancin amfanin tare da kalubalen rashin tsaro da kuma matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a wadannan nahiyoyi.

Sakamakon wannan hasashe da rahoton ya yi na samun koma baya a kan noman wadannan kayan abinci, hakan zai shafi farashin amfanin gonar kamar Masara, Alkama, Shinkafa, Gero da sauran makamantansu har nan da sama da shekaru biyar masu zuwa.

Misali, a Nijeriya idan aka yi la’akari da irin tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin kasar yake yi, rahoton ya yi hasashen samun raguwar yin noma a fadin kasar baki-daya, wanda hakan kuma zai yi sanadiyyar tashin farashin kayan abincin ya ci gaba da yin tashin gwauron zabi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

Kazalika, rahoton ya yi hasashen cewa, za a samu matukar raguwa wajen noman Shinkafa, Masara, Dawa da kuma Gero. Bugu da kari kuma, za a samu raguwar noman amfanin gona a Nijeriya da Nijar da Chadi da kuma Mali.

Har ila yau, rahoton ya bayyana cewa, sakamakon kalubalen rashin tsaro da rikice-rikice, musamman a yankin Liptako-Gourma da kuma gabar Kogin Chadi, akwai yiwuwar a haramta fitar da kaya wanda Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Afirka (ECOWAS), za ta kakaba wa yankunan; wanda hakan ya jawo a watannin baya kungiyar ta kakaba wa Kasar Nijar wannan takunkumi, wanda ya yi sanadiyyar dakatar da hada-hadar zirga-zirgar gudanar da kasuwanci a tsakaninsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noman alkamaNoman GeroNoman rani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Liu Jianchao Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Next Post

Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

12 hours ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

13 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 day ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

1 week ago
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

3 weeks ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

3 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba

Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka'ida Ba

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

September 27, 2025
Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

September 27, 2025
Yadda Ake Hada Sushi

Yadda Ake Hada Sushi

September 27, 2025
Ribar Da Manyan Kamfanonin Kasar Sin Ke Samu Ta Dawo Turbar Karuwa A Watanni 8 Na Farkon Bana

Ribar Da Manyan Kamfanonin Kasar Sin Ke Samu Ta Dawo Turbar Karuwa A Watanni 8 Na Farkon Bana

September 27, 2025
Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

September 27, 2025
Tawagar Gwamnatin Tsakiya Na Ci Gaba Da Ziyartar Jami’ai Da Mazauna Yankuna Da Dama Na Jihar Xinjiang

Tawagar Gwamnatin Tsakiya Na Ci Gaba Da Ziyartar Jami’ai Da Mazauna Yankuna Da Dama Na Jihar Xinjiang

September 27, 2025
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

September 27, 2025
Hadin Tsumin Baure

Hadin Tsumin Baure

September 27, 2025
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

September 27, 2025
Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.