• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Fuskantar Koma-baya A Noman Alkama, Masara Da Gero – Rahoto

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya Na Fuskantar Koma-baya A Noman Alkama, Masara Da Gero – Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani rahoton hadaka na hasashen harkokin kasuwanci na yankin Afirka, wanda Hukumar Abinci da Aikin Gona ta Duniya (FAO), tare da shirin samar da abinci na duniya (WFP) suka wallafa a kwanan baya, an yi hasashen cewa, za a samu koma baya a bangaren noman kayan amfanin gona a Nijeriya, Nijar, Chadi da kuma Mali.

A cewar rahoton, an yi hasashen tashin farashin wadannan kayan amfanin gona a daukacin wannan nahiya, a yayin kuma da ake sa ran ci gaba da kara bukatarsu.

  • Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023
  • Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Tantuna Don ‘Yan Gudun Hijira Da Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kazalika, rahoton ya danganta afkuwar hakan a kan kalubalen hada-hadar kasuwancin amfanin tare da kalubalen rashin tsaro da kuma matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a wadannan nahiyoyi.

Sakamakon wannan hasashe da rahoton ya yi na samun koma baya a kan noman wadannan kayan abinci, hakan zai shafi farashin amfanin gonar kamar Masara, Alkama, Shinkafa, Gero da sauran makamantansu har nan da sama da shekaru biyar masu zuwa.

Misali, a Nijeriya idan aka yi la’akari da irin tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin kasar yake yi, rahoton ya yi hasashen samun raguwar yin noma a fadin kasar baki-daya, wanda hakan kuma zai yi sanadiyyar tashin farashin kayan abincin ya ci gaba da yin tashin gwauron zabi.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

Kazalika, rahoton ya yi hasashen cewa, za a samu matukar raguwa wajen noman Shinkafa, Masara, Dawa da kuma Gero. Bugu da kari kuma, za a samu raguwar noman amfanin gona a Nijeriya da Nijar da Chadi da kuma Mali.

Har ila yau, rahoton ya bayyana cewa, sakamakon kalubalen rashin tsaro da rikice-rikice, musamman a yankin Liptako-Gourma da kuma gabar Kogin Chadi, akwai yiwuwar a haramta fitar da kaya wanda Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Afirka (ECOWAS), za ta kakaba wa yankunan; wanda hakan ya jawo a watannin baya kungiyar ta kakaba wa Kasar Nijar wannan takunkumi, wanda ya yi sanadiyyar dakatar da hada-hadar zirga-zirgar gudanar da kasuwanci a tsakaninsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noman alkamaNoman GeroNoman rani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Liu Jianchao Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Next Post

Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

4 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

4 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

5 days ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

6 days ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba

Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka'ida Ba

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.