ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
Gwamnati

Gwamnatin Jihar Kogi ta zurfafa haɗin gwuiwa da hukumomin tarayya da kuma masu zuba jari na ƙasashen waje domin mayar da noma ginshiƙin a tattalin arziƙin jihar, da tabbatar da samar da wadataccen abinci da kuma fitar da amfanin gona zuwa ƙasashen waje.

Kwamishinan Noma da tsaro na abinci, Timothy Ojomah, ya bayyana haka a yayin ziyarar duba wata gona a Geregu, ƙaramar hukumar Ajaokuta, tare da ƙwararru da masu zuba jari, inda suka tattauna kan damar noman zamani da faɗaɗa kasuwa. Ya ce wannan tsari yana daidai da hangen nesa na Gwamna Usman Ododo wajen ƙarfafa manoma, samar da aiyukan yi, da kuma gina tattalin arziƙi mai ɗorewa.

  • NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

A nasa jawabin, Mai ba wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin noma, Mathew Ajayi, ya ce haɗin gwuiwar ta yi daidai da shirin Shugaba Bola Tinubu na tabbatar da tsaron abinci da rage dogaro da shigo da kayan abinci daga ƙasashen waje. Ya ce an fi karkata hankali kan shinkafa, da masara, da waken soya da wasu amfanin gona da za a iya fitarwa zuwa ƙasashen waje.

ADVERTISEMENT

Shugaban Hukumar Musayar Amfanin Gona ta Jihar Kogi, Victor Omofaiye, ya bayyana cewa hukumar za ta tabbatar da farashi mai adalci da samun damar kasuwannin waje ga manoma. A gefe guda kuma, Daraktan Onida Agri, Israel Kidron, ya ce Kogi ta dace da noman zamani saboda ƙasar ta mai albarka ce da kuma wadataccen ruwa. Ya ƙara da cewa kamfanin zai taimaka wajen horas da manoma da kawo fasahohi na zamani domin inganta amfanin gona.

Wannan haɗin gwuiwa ana sa ran zai ratsa wasu ƙananan hukumomi a jihar, inda zai samar da ayyukan yi, da ƙarfafa manoma, tare da mayar da Kogi ɗaya daga cikin manyan jihohin da ke taka rawa wajen sauya fasalin noma a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Gwamnati
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

Trump Ya Haramta Wa Jami'an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.