• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Karuwar Garkuwa Da Mutane Duk Da Hada Layukan Waya Da Lambar NIN – Pantami

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Dalilin Karuwar Garkuwa Da Mutane Duk Da Hada Layukan Waya Da Lambar NIN – Pantami
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Farfesa Isa Pantami, ya ce, rashin rungumar tsarin hada layukan waya da lambar shaidar dan kasa (NIN-SIM) ya bai wa ayyukan ta’addancin kwarin guiwar ci gaba da tsula tsiya, musamman garkuwa da mutane a fadin kasar nan.

Ministan wanda ke ba da amsa kam tambayar da wani ya yi a shafin Tiwuta mai suna Mentus da ya yi tambayar me ya sa aka tursasa ‘yan Nijeriya zuwa hada lambar wayarsu da lambar NIM da nufin dakile ayyukan ta’addanci amma har yanzu ayyukan ta’addancin na ci gaba da wakana.

  • NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

Mai tambayar ya ce me ya sa aka sanya ‘yan Nijeriya mallakar shaidar NIN? Da ba a tilasta musu ba in an san ba zai yi tasiri ba.

Tun da farko, tsohon ministan ya wallafa cewa daya daga cikin abokansa ya tara naira miliyan hamsin a matsayin gudunmawar da aka harhada domin tara naira miliyan 100 da masu garkuwa da mutane suka bukata bayan sace ‘yan mata shida a Abuja.

Ya ce, ya yi magana da mahaifin ‘yan matan biyo bayan kashe daya daga cikinsu Najeeba wacce take gab da kammala jami’a biyo bayan gaza biyan kudin fansar da mahaifin nasu ya kasa yi na biyan miliyan 60.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Pantami wanda shi ne ya kawo tsarin hada lambar NIN-SIM ya ce, kwata-kwata ba tsarin ne ke da matsala ba, illa rashin tabbatar da amfani da tsari da hukumomi da cibiyoyi suka kasa yi shi ne babban matsalar.

Ya daura alhalin rashin amfanin tsarin ga hukumomin da aka ware domin kare rayukan al’umma, inda suka yi watsi da hakan duk kuwa da cewa suna da kayan aikin da suka dace na bibiya da bin sawun masu amfani da layukan wayoyi.

“Tsarin NIN-SIM na aiki sosai. Amma, hukumomin da abun ya shafa da ke yaki da ‘yan ta’addan an bukaci su tabbatar da amfani da tsari a duk lokacin da aka aikata wani ta’addanci. Amma rashin amfani da tsarin da aiwatar da shi shi ne babban matsalar ba wai tsarin ba.

“Idan har hukumomin da suka dace ba su yi amfani da tsarin ba wajen kare rayuka da dukiyar jama’an kowani mutum to da matsala, ni na sadaukar da rayuwana na kau da kaina daga dukkanin barazanar kasheni domin tabbatar da fito da wannan tsarin,” ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Garkuwa Da Mutane Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

Next Post

Fifikon Annabi (SAW) Da Na Al’ummarsa

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

4 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

5 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

10 hours ago
Pantami
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

12 hours ago
Next Post
Fifikon Annabi (SAW) Da Na Al’ummarsa

Fifikon Annabi (SAW) Da Na Al’ummarsa

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.