• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Yadda Dalibai Za Su Samu Bashi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Ilimi
0
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana yadda dalibai za su samu bashi karkashin shirin da ta bullo da shi domin tallafa musu wajen gudanar da karatunsu cikin sauki.

A cewar gwamnatin tarayya, shirin zai gudana ne a zamance ba sai daliban sun sha wata wahala wajen samun wannan bashi ba.

  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024
  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024

Babban sakataren shirin bai wa dalibai bashi na kasa, Dakta Akintunde Sawyerr shi ya bayyana hakan a fadar shugaban kasa jim kadan bayan sun kammala ganawa da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, wanda ya bayyana masa cewa an samu nasarar taura kudaden bai wa dalibai bashi a asusun makarantu.

Shirin zai kuma bai wa matasan Nijeriya daman samun horon sana’o’I bayan kammala makarantun gaba da sakandare.

Sawyerr ya yi wannan bayani ne ga manema labarai tare da shugaban hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS), Dakta Zacch Adedeji.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Shi me Dakta Adedeji ya tofa albarkacin bakinsa, inda ya bayyana cewa sun gana da shugaban kasa ne saboda harajin ilimi shi ne babban hanyar samun kudin da za a bai wa dalibai bashi.

Sawyerr ya kara da cewa shirin zai taimaka wa dalibai wajen bangaren sana’ar da suke burin cimmawa, maimakon tilasta musu kan wani lamari saboda karancin kudade wajen gudanar da harkokin karatu.

Ya tabbatar da cewa shirin zai taimaka matuka gaya na hatsarin da matasan Nijeriya ke fadawa lokacin da suke yunkurin shiga kasashen Turai domin samun rayuwa mai inganci.

Sawyerr ya ce, “Mun yi tunani sosai kafin fara wannan shirin. Idan har dalibai ya bukaci wannan bashi, to ba sai ya hadu da wani mutum ba. Akwai manhaja da dalibi zai shiga wajen neman bashin.

“Ko wani dalibi da ke sha’awar amsar bashin kwai zai shiga manhajan ne sai ya cika abubuwan da ake bukata domin samun cikakken bayaninsa. Abubuwan da ake bukata sun hada da lambar jarrabawar shiga manyan makaranta da bangaren da yake karatu da kuma ranar haihuwa.

“Sauran sun hada da lambar dan kasa wanda zai tabbatar da cewa shi dan Nijeriya ne, domin bashin ana bai wa daliban Nijeriya ne kadai. Katin dan kasa zai taimaka mana wajen bayyana sahihancin bayanan dalibi. Sannan ana bukatar lambar BBN, wannan zai taimaka wajen sanin asusun dalibi.

“An kirkiri wannan shirin ne domin tallafa wa daliban Nijeriya wadanda ba za su iya biyan kudin makaranta ba, sannan kuma zai taimaka musu wajen samun sana’oin dogaro da kai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Bukaci Sin Da Faransa Su Hada Hannu Wajen Bude Hanyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Domin Kyautata Rayuwar Bil Adama

Next Post

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

Related

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

1 day ago
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE
Ilimi

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

1 week ago
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO
Ilimi

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

2 weeks ago
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe
Ilimi

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

3 weeks ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

4 weeks ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

4 weeks ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.