ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Yadda Dalibai Za Su Samu Bashi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Dalibai

Gwamnatin tarayya ta bayyana yadda dalibai za su samu bashi karkashin shirin da ta bullo da shi domin tallafa musu wajen gudanar da karatunsu cikin sauki.

A cewar gwamnatin tarayya, shirin zai gudana ne a zamance ba sai daliban sun sha wata wahala wajen samun wannan bashi ba.

  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024
  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024

Babban sakataren shirin bai wa dalibai bashi na kasa, Dakta Akintunde Sawyerr shi ya bayyana hakan a fadar shugaban kasa jim kadan bayan sun kammala ganawa da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, wanda ya bayyana masa cewa an samu nasarar taura kudaden bai wa dalibai bashi a asusun makarantu.

ADVERTISEMENT

Shirin zai kuma bai wa matasan Nijeriya daman samun horon sana’o’I bayan kammala makarantun gaba da sakandare.

Sawyerr ya yi wannan bayani ne ga manema labarai tare da shugaban hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS), Dakta Zacch Adedeji.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Shi me Dakta Adedeji ya tofa albarkacin bakinsa, inda ya bayyana cewa sun gana da shugaban kasa ne saboda harajin ilimi shi ne babban hanyar samun kudin da za a bai wa dalibai bashi.

Sawyerr ya kara da cewa shirin zai taimaka wa dalibai wajen bangaren sana’ar da suke burin cimmawa, maimakon tilasta musu kan wani lamari saboda karancin kudade wajen gudanar da harkokin karatu.

Ya tabbatar da cewa shirin zai taimaka matuka gaya na hatsarin da matasan Nijeriya ke fadawa lokacin da suke yunkurin shiga kasashen Turai domin samun rayuwa mai inganci.

Sawyerr ya ce, “Mun yi tunani sosai kafin fara wannan shirin. Idan har dalibai ya bukaci wannan bashi, to ba sai ya hadu da wani mutum ba. Akwai manhaja da dalibi zai shiga wajen neman bashin.

“Ko wani dalibi da ke sha’awar amsar bashin kwai zai shiga manhajan ne sai ya cika abubuwan da ake bukata domin samun cikakken bayaninsa. Abubuwan da ake bukata sun hada da lambar jarrabawar shiga manyan makaranta da bangaren da yake karatu da kuma ranar haihuwa.

“Sauran sun hada da lambar dan kasa wanda zai tabbatar da cewa shi dan Nijeriya ne, domin bashin ana bai wa daliban Nijeriya ne kadai. Katin dan kasa zai taimaka mana wajen bayyana sahihancin bayanan dalibi. Sannan ana bukatar lambar BBN, wannan zai taimaka wajen sanin asusun dalibi.

“An kirkiri wannan shirin ne domin tallafa wa daliban Nijeriya wadanda ba za su iya biyan kudin makaranta ba, sannan kuma zai taimaka musu wajen samun sana’oin dogaro da kai.”

Dalibai
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.