• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangantaka Tsakanin Nijeriya da Sin Ta Kara Karfi Yayin Da Jirgi Ya Fara Tashi Zuwa Guangzhou

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Dangantaka Tsakanin Nijeriya da Sin Ta Kara Karfi Yayin Da Jirgi Ya Fara Tashi Zuwa Guangzhou
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dangantakar kasuwanci tsakanin Nijeriya da kasar Sin ta kara karfi, bayan kaddamar da zirga-zirgar jiragen sama na kasuwanci da kamfanin jiragen sama na Air Peace, ya yi zuwa birnin Guangzhou na kasar Sin.

A ranar Laraba ne kamfanin Air Peace ya fadada jigila zuwa Asiya tare da fara zirga-zirgar jiragen sama kai tsaye na mako guda zuwa kasar Sin.

  • Kiristoci Kada Su Damu Da Takarar Musulmi 2 – Shugaban Jam’iyyar APC
  • Mata 700,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sanadin Dajin Mama

Jirgin da ya tashi da misalin karfe 22:00 na da jimillar fasinjoji 240 wadanda aka yi ta daga sabuwar tashar da aka kaddamar kai tsaye zuwa kasar Sin ta jirginsa Boeing 777.

Kazalika, kamfanin ya bayyana cewa, ana shirin hada biranen Beijing, da Shanghai da sauran biranen Nijeriya, ta hanyar yin amfani da tsarin layin dogo da wani kamfanin jiragen sama na Asiya.

Da take jawabi yayin kaddamar da jirgin, babbar jami’ar gudanarwa na kamfanin Air Peace, Oluwatoyin Olajide, ta bayyana cewa, kamfanin ya yi hasashen kamfanin zai samar da dimbin ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya da kuma rage wa ‘yan Nijeriya nauyin tafiye-tafiyen jiragen sama, da kuma sauran ‘yan Afirka ta hanyar samar da ayyukan yi na hadin kai mai araha da lumana a cikin birane da nahiyoyi.

Labarai Masu Nasaba

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Ta ce: “Yanzu, za mu iya tabbatar da cewa Air Peace ya yi wannan hangen nesa don fadada hanyar sadarwar da ake da su don biyan bukatun tafiye-tafiye a sama na jama’a masu. A yau, muna kara kaimi zuwa nahiyar Asiya a hukumance, tare da fara jigilar jirgin farko na mako guda zuwa Guangzhou-Si .

“Idan har kuna bibiyar ci gaban da kamfani na Air Peace ke yi, za ku san cewa sararin samaniyar kasar Sin ba sabon abu ba ne a gare mu, domin mun samu nasarar gudanar da jigilar jiragen sama na musamman zuwa kasar a lokuta daban-daban a baya, musamman a 2020, lokacin kullen Korona.

“Don haka, za mu shiga kasar Sin, ba a matsayin sababbi ba, amma a matsayin kamfanin jirgin sama wanda ya kware a fannin fasaha da aiki tare da kasar Sin. Jama’a masu tashi, musamman ma wadanda ke tashi daga hanyar Guangzhou, ya kamata su yi tsammanin kwarewar jirgin sama mafi inganci, wanda ke da alama ta Air Peace.

“Ba mu tsaya a iya Guangzhou ba – Indiya ce ta gaba kuma Isra’ila ma na cikin tsarinmu. Haka kuma ana shirin kaddamar da aikinmu a Malabo a Equatorial Guinea da Kinshasa a Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo.

“Za mu ci gaba da habaka hanyoyin sadarwarmu tare da sabunta dabaru. Air Peace a halin yanzu yana alfahari da hanyar sadarwa na hanyoyin cikin gida guda ashirin, hanyoyin yanki guda bakwai da wurare biyu na duniya, ciki har da Dubai da Johannesburg.”

Olajide, wadda ta amince da rawar da hukumomin gwamnati da ma’aikatar sufurin jiragen sama suka taka wajen cimma nasarar, ta ce adadin jigilar zai karu da zarar hukumomin kasar Sin sun sassauta dokokin Korona.

A cewarta, jirgin zai kara dankon zumunci tsakanin Nijeriya da Sin duk da cewar kasashen biyu za su ci gajiya sosai daga ayyukansu na jiragen kai tsaye.

Ta ce, “yau za mu fara jigilar jirgin mu na farko kai tsaye zuwa kasar Sin, idan muka yi la’akari da yawan al’ummar Sinawa a Nijeriya da aikin da suke yi wa Nijeriya, za mu iya tunanin irin tasirin da ya yi kan tattalin arziki. Don haka, idan za mu yi jigilar kai tsaye tsakanin Nijeriya zuwa kasar Sin, hakan zai karfafa dankon zumuncin da ke tsakanin kasashen biyu, zai kuma kara samun kudaden shiga da ake samu daga cudanya da tattalin arzikin kasashen biyu.

“Wannan dangantaka ce da Air Peace ta samu damar samarwa sannan kuma muna fatan ta zama babbar fa’ida.

Ta kara da cewa, “Yayin da muke fara jigilar Guangzhou a yau, dole ne mu yaba wa hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Nijeriya, NCAA, hukumar kula da filayen jiragen sama ta Nijeriya, FAAN, ma’aikatar sufurin jiragen sama, gwamnatin kasar Sin, abokan huldarmu, da sauran masu ruwa da tsaki kan tabbatuwar hakan. Mun yi alkawarin yin aiki cikin jituwa tare da kowa don tabbatar da cewa an inganta wannan sabuwar tafiya. ”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Air PeaceBirnin GuangzhouIndiyaJigilaNijeriyaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kiristoci Kada Su Damu Da Takarar Musulmi 2 – Shugaban Jam’iyyar APC

Next Post

Kwankwaso Ya Zabi Fasto Mataimakinsa A Zaben 2023

Related

Air Peace
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

3 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

3 hours ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

4 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

4 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 19-09-2025

5 hours ago
Air Peace
Labarai

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

6 hours ago
Next Post
kwankwaso

Kwankwaso Ya Zabi Fasto Mataimakinsa A Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

Air Peace

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Air Peace

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.