Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP Sanata Rabiu Kwankwaso, ya zabi Bishop Isaac Idahosa a matsayin mataimakinsa a zaben 2023 mai zuwa.
Jam’iyyar ta bayyana hakan ne a shafinta na Twitter a ranar Alhamis.
Fasto Bishop Isaac Idahosa dan asalin jihar Edo ne.
ADVERTISEMENT
Idahosa babban Fasto ne na God First Ministry, wanda aka fi sani da Illumination Assembly, wanda ke da hedikwatarsa a Lekki Light Center (LLC), Ajah, Legas. Rahoton Tribune
A dakace mu da cikakkun bayanai na tafe.














