• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Karɓo Sakamakon Jarabawar WAEC Da Hukumar Ta Riƙe

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Karɓo Sakamakon Jarabawar WAEC Da Hukumar Ta Riƙe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙoƙarin da ya ke yi don ganin ya cika alƙawuran da ya yi wa Zamfarawa, musamman a harkar ilimi, Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya samu nasarar karɓo sakamakon jarabawar WAEC na ‘yan asalin jihar, wanda Hukumar ta ƙi saki saboda rashin biyan kuɗin jarabawar.

Ita dai Hukumar da ke kula da shirya jarabawar ta WAEC ta riƙe sakamakon jarabawar ɗaliban jihar Zamfarar ne sakamakon bashin Naira Biliyan 1.4 da ta ke bin gwamnatocin jihar da suka gabata.

  • Zannan Bungudu Ya Gina Masallatai 20 Makarantun Islamiyya 15 A Jihar Zamfara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin ‘Pulaku’ Don Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawu Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa Gwamnan ya samu ganawa da shugabannin Hukumar ne a ofishin sa da ke Abuja ranar Litinin da ta gabata.

Ya ce, a ziyarar da suka kawo wa Gwamnan, sun samu ganawa da shugabannin Hukumar bisa jagorancin shugabar sashen mulki da harkokin kuɗi, Hajiya Binta Abdulkadir da kuma shugaban ofishin WAEC, Dr. Amos J. Dangut.

Ya ci gaba cewa, “A ƙoƙarin da gwamnatin nan ke yi na ganin ta haƙƙaƙa shirin ta na sanya dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, Gwamna Dauda Lawal ya karɓi baƙuncin Shugabannin Hukumar WAEC a ofishin sa da ke Abuja.

Labarai Masu Nasaba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

“Gwamnan, wanda ke tare da Kwamishinan ilimi, kimiyya da fasaha, Mallam Wadatau Madawaki, sun tattauna da shugabbanin Hukumar ta WAEC a kan abin da ya shafi basussukan da ake bin jihar Zamfara na gwamnatocin da suka gabata.

“Rashin biyan waɗannan kuɗaɗe na tsawon shekaru ya sa hukumar ta ƙi bayyana sakamakon jarabawar ɗaliban jihar suka zana, wanda wannan yanayi ya jawo wa ɗaliban da suka kammala Jami’o’i rashin zuwa yi wa ƙasa hidima na NYSC saboda rashin sakamakon na WAEC a hannun su.

Sanarwar ta Idris ta ƙara da bayyana cewa, a wancan zaman, an cimma matsaya tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Hukumar ta WAEC kan yadda za a shawo kan lamarin bashin.

“A ƙarshen zaman, Hukumar ta amince za ta fitar da sakamakon jarabawar da suka gabata, tare da amincewa ɗaliban jihar za su zauna don zana jarabawar WAEC ta shekarar 2024.

“Duk ɓangarorin byu sun amince da tsarin da aka yi na biyan bashin da ake bi, tare da cewa za a saki sakamakon jarabawar kafin ƙarshen watannan.”

A wannan ganawa dai, akwai manyan ma’aikatan Hukumar, waɗanda suka haɗa da Mr Ambrose Okelezo, shugaban shiyya; Mr Victor C. Odu, Daraktan kuɗi; da Mr Segun U. Jerumeh, Mataimakin Darakta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana’antar Kera Jiragen Ruwa Ta Sin Ta Samu Karin Riba A Shekarar Bara

Next Post

Tinubu Zai Halarci Taron AU Karo Na 37 A Birnin Addis Ababa Na Kasar Habasha

Related

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

15 minutes ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

2 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

3 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

4 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

6 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

8 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Isa Birnin New York Don Halartar Taron Majalisar Dinkin Duniya A Karo Na Farko

Tinubu Zai Halarci Taron AU Karo Na 37 A Birnin Addis Ababa Na Kasar Habasha

LABARAI MASU NASABA

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.