Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja, ta yi barazanar kwace filaye 9,671 ga wadanda ba su biya harajin filaye na shekarar 2023 a cikin makwanni biyu masu zuwa ba.
Wadanda ke sahun gaba da ba su biya harajin ba sun hada da; ofisoshin jakadancin kasashen waje, wadanda ake bin su kimanin dala miliyan 5.3.
- Da Ɗumi-ɗumi: Bayan CBN, FAAN, Manyan Ma’aikatun Hukumar Man Fetur Na Shirin Komawa Legas
- Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Kammala Gwajin Tashi Da Sauka A Yanayin Hunturu
Kamar yadda sanarwar ta bayyana, sai kuma kamfanoni da sauran daidaikun mutanen da ake bin su kudin harajin kimanin Naira 2,205,079,937.
Har ila yau, Hukumar Babban Birnin Tarayyar, a cikin kunshin sanarwar ta kara da cewa, ta na kara tunatar da wadanda suka mallaki wurare a Abujan; wajen ci gaba da biyan harajin da doka ta tanadar a kan duk wanda ya mallaki fili, sannan za a iya biyan wannan haraji tun kafin lokacin biyan ma ya yi.
Haka zalika, Ministan Abuja Nyesom Wike, ya nemi shugabanni da sauran wadanda suka mallaki wurare daban-daban a fadin babban birnin tarayyar, da su gaggauta biyan harajin da dokar ta tilasta musu biya, domin aiwatar da ayyukan raya kasa a ciki da sauran kewayen na Abuja.
Ministan ya yi wannan kira ne, a lokacin gudanar da duba ayyukan da ake aiwatarwa; ciki har da gidan Mataimakin Shugaban Kasa, wanda a halin yanzu Kamfanin Julius Berger ke kan ginawa a Asokoro da kuma aikin shataletalen da ake kan yi a ‘Area 1’, wanda Kamfanin CGC ke ginawa duk dai a babban birnin tarayyar.
Sannan akwai aikin gada na Wuye, wanda shi ma a halin yanzu ake kan aikinsa ka’in da na’in karkashin Kamfanin Arab da kuma titin D6 da B12, wanda shi ma Kamfanin Julius Berger ne ke aiwatar da shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp