• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kalla yara dari hudu, marayu da masu karamin karfi daga kananan hukumomi shida na jihar Kebbi ne suka samu tallafin karatu daga Gidauniyar M-TECH, ta hanyar ba su fom din JAMB kyauta tare da biyan dukkan kudaden karatu ga wadanda suka ci jarabawar tantancewar da aka gudanar a dukkan jami’o’in ko kuma kwalejin da ke fadin jahohin kasar nan.

Shugaban Gidauniyar M-TECH, Alhaji Manir Musa Jega, ya bayyana cewa an zabo matasa marasa galihu ne bisa aikin tantancewa da aka yi da nufin samun mabukata na gaskiya ko kuma marasa galihu su iya samun wannan tallafin karatu a kyauta da gidaumiyata ta M-TECH ke bayarwa.

  • Alamomin Cutar Shan Inna Sun Bulla A Kananan Hukumomi 9 Na Jihar Kebbi
  • Gwamnatin Kebbi Ta Kaddamar da Aikin Gina Tashar Motoci Ta Zamani A Birnin Kebbi

Kazalika, ya kara da cewa” Gidauniyar na ba su fom din JAMB kyauta da guraben karo ilimi amma ba su da mai taimaka musu da kudi don ci gaba da karatunsu a manyan makarantun da ke fadin jihohin kasar nan. Bisa ga hakan ne gidauniyar M-TECH ke taimakawa don ganin cewa ‘ya’yan marasa galihu ko marayu sun ci gaba da kararunsu a manyan makarantun kasar nan, inji Injiniya Manir Jega”.

Ya ce “mutanen da aka zabo sun fito ne daga kananan hukumomi shida na jihar da suka ci gajiyar tallafin, kuma sun hada da kanana hukumomin Birnin Kebbi da Jega da Bunza da Maiyama da Aliero da Gwandu. Haka kuma an gudanar da wata jarrabawar tantancewa don a zaɓi mafi kyawun su, inji Shugaban gidauniyar M-TECH Injiniya Manir Jega”.

A cewarsa, don karfafa musu gwiwa ne ta hanyar ba su tallafin karatu kuma gidauniyata ta M-TECH ta kafa cibiyar mock ta UTME domin sanar da su dabarun na’ura mai kwakwalwa domin samun nasarar rubuta jarabawar ta kwamfuta. Ya kara da cewa wadanda suka yi nasara za a biya musu kudaden tallafin karatu a cikin manyan makarantun da suka zaba na jahohin kasar Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Har ilayau, Injiniya Manir Jega yana kira ga masu hannu da shuni a cikin al’umma da su taimaka wa masu karamin karfi da wadanda suke da kuduri aniyar yin karatu amma iyayensu ba sa raye ko kuma ba su da karfin kudi don daukar nauyin karatun su.

Ya kuma yabawa Gwamnan jihar Kebbi, Kwamared Dakta Nasir Idris bisa yadda ya zuba jari sosai a fannin ilimi a cikin watanni takwas kacal a kan karagar mulki da ma sauran sassan don ci gaban al’ummar jihar.

Ya kuma yi kira ga al’umma a fadin jihar da su ci gaba da baiwa gwamnati mai ci yanzu goyon baya da nufin samun rabon dimokuradiyya tare da yin addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Next Post

Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

1 hour ago
Kebbi
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

3 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

6 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

9 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

9 hours ago
Next Post
Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

LABARAI MASU NASABA

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kebbi

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.