• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wata Kasa Da Za Ta Tsira Muddin Akasarin Kasashen Duniya Na Cikin Tashin Hankali 

by CGTN Hausa
2 years ago
Kasashen duniya

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi kira da a yi kokarin kaucewa ra’ayin tafka asara, yayin da yake karin haske kan rahoton shekara-shekara da aka fitar gabanin kammala taron tsaro na Munich, wanda ya bayyana damuwa kan karuwar ra’ayin tabka asara. 

A yayin da ake fuskantar karuwar tabarbarewar al’amuran duniya da suka haifar da kuncin rayuwa ga tarin al’ummomi, har yanzu wasu kasashe sun fi mayar da hankali kan rungumar ra’ayin cin riba daga faduwar wata kasa. Abun da har yanzu wasu kasashe suka gaza fahimta shi ne, babu wata kasa da za ta samu kwanciyar hankali muddun akasarin kasashen duniya na fama da tashin hankali ko rashin tsaro ko talauci.

  • Ya Kamata Kasashen Yamma Su Ji Shawarwarin Kasar Sin Maimakon “Damuwa Da Asara”
  • Wang Yi Ya Yi Tir Da Karairayin Da Ake Yi Game Da Xinjiang A Munich

Abun kunya ne da takaici, a ce manyan kasashe sun zama masu cin riba daga asarar kananan kasashe maimakon zama abun dogaro ko wadanda ke tallafawa domin ganin ci gaban kasashen dake musu kallon ababen koyi.

Kamar yadda Wang Yi ya bayyana, bangaren kasar Sin ya yi imanin cewa, ra’ayin cin moriya da faduwar wani, da neman mayar da wasu saniyar ware, da yunkurin yin fito-na-fito na wani gungu, su ne ke haifar da ra’ayin “tabka hasara”.

To ina mafita?

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kamar dai yadda kullum kasar Sin ke kira, mafitar ita ce tabbatar da daidaito tsakanin kasa da kasa ta hanyar inganta hulda da cudanya a tsakaninsu bisa gaskiya da adalci. Idan dai za a kyautata hulda bisa gaskiya da sanin ya kamata, to tabbas babu wani bangare da zai so ganin faduwar abokan huldarsa. Ya kamata a hada karfi da karfe don a gudu tare a tsira tare.

Yanayin da duniya ta shiga, ko in ce wasu tsirarun kasashe suka jefa duniya ciki, ta shaida cewa, idan har ba a dawo kan turbar da ta dace ta daidaito da adalci ba, to ba za a samu kyakkyawar makomar da ake buri ba.

Kasar Sin mai rajin ganin an samu ci gaba da tabbatuwar adalci da cudanya da hadin gwiwar bangarori daban daban, ita kadai ba za ta iya tabbatar da hakan ba. Dole manyan kasashe su mara mata baya, su ba da gudunmawarsu bil hakki da gaskiya, su ajiye girman kai da hadama, a hada hannu a ceto duniya daga durkushewa. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 
Daga Birnin Sin

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Next Post
Kwastam Za Ta Raraba Wa ‘Yan Nijeriya Shinkafa Da Sauran Kayan Da Ta Kwato

Kwastam Za Ta Raraba Wa 'Yan Nijeriya Shinkafa Da Sauran Kayan Da Ta Kwato

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

October 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.