• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Yadda Lamarin Ke Rincabe Wa Almajira Da Mabarata

by Sani Anwar
1 year ago
in Labarai
0
Tsadar Rayuwa: Yadda Lamarin Ke Rincabe Wa Almajira Da Mabarata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk wanda ya kwana ya tashi a wannan kasa, yana cike da sanin yadda tsadar rayuwa ke ci gaba da ta’azzara, musamman a bangaren da ya shafi kayan abinci da sauran kayan masarufi.

A kullum ta Allah, idan magidanci ya je kasuwa; sai ya yi kamar ya sa hannu a ka ya ce wayyo Allah, sakamakon farashin yau daban na gobe daban.

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 
  • Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

Yana da matukar wuya a cikin irin wannan hali da ake ciki a samu magidancin da ya ke iya dora tukunya a gidansa sau uku a rana, ko da kuwa an samu damar dora tukunyar, watakila sau biyu ne ko sau daya.

Akwai magidanta da dama da suke sanya wa almajirai kwano a gidajensu, a ba su abinci da safe da rana da kuma dare, amma wannan hali da aka tsinci kai a ciki; ya dagula al’amura baki-daya.

Domin kuwa a yanzu, kusan kowa takansa ya ke yi, an koma halin nafsi-nafsi; wanda ko shakka babu Almajirai masu Allah ya ba ku mu samu, suna matukar dandana kudarsu.

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Al’amarin da ya sa Almajiran suka gane cewa, lallai yanzu fa al’amuran sun canza, wannan kuma ya fara ne tun daga 29 ga Mayun 2023, bayan da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya cire tallafin mai, ba tare da wani bata lokaci ba farashin kaya ya fara tashi, tun ana ganin abin kamar wasa, har aka kawo wannan hali da ake ciki yanzu, domin kuwa kullum farashin kara tashin gwauron zabo ya ke yi.

Shi yasa Almajirai abin ya yi musu matukar wuya, su ma suke ji a jikinsu; musamman wadanda a da idan an ba su sadakar abincin da bai yi musu ba, kamar tuwo da sauransu sai su samu gefen kwata su zubar.

Guda daga cikin ire-iren wadannan Almajirai da abokansa suke tuna masa da irin wulakancin da suka rika yi wa tuwo a ‘yan shekarun da suka gabata, fashewa ya yi da kuka, inda su da kansu suke alakanta wulakancin da suka yi wa abincin da kuma wannan hali da suka samu kansu na rashin samun abincin akai-akai a halin yanzu a ciki.

Hausawa na fadin cewa, duk bakin da Allah ya tsaga; ba ya hana shi abinci ko da kuwa babu dadi. Wannan magana ta Bahaushe, ko shakka babu; haka ta ke babu wani gyara a ciki, domin kuwa ba mutum ba ko dabbar da Allah ya halitta, ba ya hana ta abin da za ta kai baki.

Har ila yau, wannan tsadar rayuwa da ake fama da ita, ya sa wasu daga cikin jihohi; musamman a Arewa, fara yin bore ta hanyar aiwatar da zanga-zanga, domin nuna rashin amincewarsu da halin da suka tsinci kansu a ciki.

Koda-yake, a hannu guda kuma, shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya nuna damuwarsa tare da sanya dokar ta-baci, a kan harkokin noma; inda gwamnatinsa ta sha alwashin sama wa ‘yan Nijeriya wadataccen abinci, ta yadda har sai an samu rarar da za a rika fita da shi zuwa kasashen waje.

Haka nan, su ma gwamnoni daga jihohi daban-daban, sun yi yunkurin daukar matakai; musamman a bangaren da ya shafi kayan abinci, duk dai don rage wa al’umma radadin wannan hali da suke ciki.

A nan, muna sake yin kira ga gwamnatin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi da su sake jajircewa tare da mayar da hankali a kan wadannan matsaloli da ke addabar wannan kasa tun kafin kan talakawa ya kwace, su fito su fara yin abin da ba shikenan ba.

Dalili kuwa shi ne, akwai wadanda su ke ganin cewa, duk duniya babu wanda ya kai talakan  Nijeriya hakuri da juriya, domin kuwa ya jure rashin wutar lantarki da rashin hanyoyi da matsalar lafiya da ilimi da ruwan sha da sauran makamantansu, amma ga dukkan alamu an kusa zuwa inda hakurin nasa zai tike.

Saboda haka, yanzu dai shawara ta rage ga mai shiga rijiya, ko dai gwamnati ta yi abin da ya dace, ko kuma a nan gaba ta yi kuka da kanta. Domin kuwa, duk wanda zai sha inuwar gemu; bai kai makogwaro ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Hada Hannu Da Maharba Wajan Samar Da Zaman Lafiya A Adamawa -Rundunar Soja ta 23

Next Post

Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

2 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 hour ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
Rayuwa
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Rayuwa

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.