• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Halaka Mutane A Chadi Bayan Yunkurin Kashe Shugaban Kotun Koli

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
An Halaka Mutane A Chadi Bayan Yunkurin Kashe Shugaban Kotun Koli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Chadi ta ce an kashe mutane da dama bayan wasu mutane dauke da makamai, wadanda ake zargin ‘yan jam’iyyar adawa ta ‘Socialist Party without Borders’ ne suka kai wa hukumar tsaron kasar hari.

Ministan sadarwa Abderaman Koulamallah ya fada a ranar Talata cewa, hakan ya biyo bayan yunkurin kashe shugaban kotun kolin kasar, yana mai zargin sakataren kudi na jam’iyyar adawa ta ‘Socialist Party without Borders’ da hannu a shirin.

  • Shirin Gwamnati Na Samar Da Mafi Karancin Albashi
  • Wa’adin Da Gwamna Kano Ya Dauka Na Yi Wa Kwamishinoni Hisabi Ya Cika: Kila Wasu Za Su Karbi Littafinsu A Hannun Hagu

An kama jami’in jam’iyyar da ake zargi amma a ranar Talata, kuma ‘yan jam’iyyarsa sun ce “an kashe shi”.

Gwamnatin ta ce ta kama wasu da dama da suka kai harin, yayin da ake ci gaba da neman sauran amma kuma babu tabbas kan cewa an kama shugaban jam’iyyar, Yaya Dillo, amma a wani sako da ya wallafa a Facebook da safiyar Laraba, ya ce sojoji sun kewaye su.
Wannan na zuwa ne mako guda bayan da shugaban kotun kolin ya bayyana cewa an kai wa ofishinsa hari.

A halin yanzu jami’an tsaro na sintiri a titunan N’Djamena, yayin da al’ummar kasar suka shiga cikin fargaba.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

A wani ci gaban labarin kuma, a ranar 6 ga watan Mayu ne za a gudanar da zaben shugaban kasar Chadin wanda zai kawo karshen mulkin soji na shekaru uku da aka soma bayan shugaba Mahamat Idriss Deby Itno ya hau karagar mulki bayan rasuwar mahaifinsa a shekarar 2021.

Shugaban hukumar zaben kasar Ahmed Bartchiret, ya bayyana muhimman ranakun da za a gudanar da zaben shugaban kasar a lokacin da yake ganawa da manema labarai a Babban Birnin Kasar, N’Djamena, kamar yadda shafin intanet na Tchadinfos mai zaman kansa ya ruwaito.

Bartchiret ya jaddada muhimmancin gudanar da zaben kafin lokacin damina, inda ya bukaci abokan huldar fasaha da na kudi da su ba da hadin kai ga shirin zaben kasar.

Yayin da har yanzu shugaba Deby bai bayyana sake tsayawa takara ba a hukumance, ‘yan adawa sun bukaci da kada ya sake neman wani wa’adi.

Deby, mai shekaru 38, ya yi alkawarin shirya zabuka cikin watanni 18 bayan ya dare kan karagar mulki a watan Afrilun 2021.

Duk da haka, gwamnatinsa ta soji ta ci gaba da rike madafun iko, inda ta kara wa’adin mulkinta da karin watanni 18.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Kasar Sin Dake Geneva Ya Nanata Kira Da A Tsagaita Bude Wuta Cikin Gaggawa A Gaza

Next Post

Matasa Jami’An Sin Za Su Sauke Nauyin Ci Gaba Da Raya Tsarin Mulki Na Gurguzu Mai Sigar Musamman Ta Kasar

Related

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
Labarai

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

27 minutes ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

11 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

12 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

17 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

19 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

19 hours ago
Next Post
Matasa Jami’An Sin Za Su Sauke Nauyin Ci Gaba Da Raya Tsarin Mulki Na Gurguzu Mai Sigar Musamman Ta Kasar

Matasa Jami’An Sin Za Su Sauke Nauyin Ci Gaba Da Raya Tsarin Mulki Na Gurguzu Mai Sigar Musamman Ta Kasar

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

August 2, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.