• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Halaka Mutane A Chadi Bayan Yunkurin Kashe Shugaban Kotun Koli

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
An Halaka Mutane A Chadi Bayan Yunkurin Kashe Shugaban Kotun Koli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Chadi ta ce an kashe mutane da dama bayan wasu mutane dauke da makamai, wadanda ake zargin ‘yan jam’iyyar adawa ta ‘Socialist Party without Borders’ ne suka kai wa hukumar tsaron kasar hari.

Ministan sadarwa Abderaman Koulamallah ya fada a ranar Talata cewa, hakan ya biyo bayan yunkurin kashe shugaban kotun kolin kasar, yana mai zargin sakataren kudi na jam’iyyar adawa ta ‘Socialist Party without Borders’ da hannu a shirin.

  • Shirin Gwamnati Na Samar Da Mafi Karancin Albashi
  • Wa’adin Da Gwamna Kano Ya Dauka Na Yi Wa Kwamishinoni Hisabi Ya Cika: Kila Wasu Za Su Karbi Littafinsu A Hannun Hagu

An kama jami’in jam’iyyar da ake zargi amma a ranar Talata, kuma ‘yan jam’iyyarsa sun ce “an kashe shi”.

Gwamnatin ta ce ta kama wasu da dama da suka kai harin, yayin da ake ci gaba da neman sauran amma kuma babu tabbas kan cewa an kama shugaban jam’iyyar, Yaya Dillo, amma a wani sako da ya wallafa a Facebook da safiyar Laraba, ya ce sojoji sun kewaye su.
Wannan na zuwa ne mako guda bayan da shugaban kotun kolin ya bayyana cewa an kai wa ofishinsa hari.

A halin yanzu jami’an tsaro na sintiri a titunan N’Djamena, yayin da al’ummar kasar suka shiga cikin fargaba.

Labarai Masu Nasaba

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

A wani ci gaban labarin kuma, a ranar 6 ga watan Mayu ne za a gudanar da zaben shugaban kasar Chadin wanda zai kawo karshen mulkin soji na shekaru uku da aka soma bayan shugaba Mahamat Idriss Deby Itno ya hau karagar mulki bayan rasuwar mahaifinsa a shekarar 2021.

Shugaban hukumar zaben kasar Ahmed Bartchiret, ya bayyana muhimman ranakun da za a gudanar da zaben shugaban kasar a lokacin da yake ganawa da manema labarai a Babban Birnin Kasar, N’Djamena, kamar yadda shafin intanet na Tchadinfos mai zaman kansa ya ruwaito.

Bartchiret ya jaddada muhimmancin gudanar da zaben kafin lokacin damina, inda ya bukaci abokan huldar fasaha da na kudi da su ba da hadin kai ga shirin zaben kasar.

Yayin da har yanzu shugaba Deby bai bayyana sake tsayawa takara ba a hukumance, ‘yan adawa sun bukaci da kada ya sake neman wani wa’adi.

Deby, mai shekaru 38, ya yi alkawarin shirya zabuka cikin watanni 18 bayan ya dare kan karagar mulki a watan Afrilun 2021.

Duk da haka, gwamnatinsa ta soji ta ci gaba da rike madafun iko, inda ta kara wa’adin mulkinta da karin watanni 18.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Kasar Sin Dake Geneva Ya Nanata Kira Da A Tsagaita Bude Wuta Cikin Gaggawa A Gaza

Next Post

Matasa Jami’An Sin Za Su Sauke Nauyin Ci Gaba Da Raya Tsarin Mulki Na Gurguzu Mai Sigar Musamman Ta Kasar

Related

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

55 minutes ago
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

2 hours ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

3 hours ago
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 
Labarai

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

4 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

7 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

9 hours ago
Next Post
Matasa Jami’An Sin Za Su Sauke Nauyin Ci Gaba Da Raya Tsarin Mulki Na Gurguzu Mai Sigar Musamman Ta Kasar

Matasa Jami’An Sin Za Su Sauke Nauyin Ci Gaba Da Raya Tsarin Mulki Na Gurguzu Mai Sigar Musamman Ta Kasar

LABARAI MASU NASABA

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.