ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Halaka Mutane A Chadi Bayan Yunkurin Kashe Shugaban Kotun Koli

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Chadi

Gwamnatin Chadi ta ce an kashe mutane da dama bayan wasu mutane dauke da makamai, wadanda ake zargin ‘yan jam’iyyar adawa ta ‘Socialist Party without Borders’ ne suka kai wa hukumar tsaron kasar hari.

Ministan sadarwa Abderaman Koulamallah ya fada a ranar Talata cewa, hakan ya biyo bayan yunkurin kashe shugaban kotun kolin kasar, yana mai zargin sakataren kudi na jam’iyyar adawa ta ‘Socialist Party without Borders’ da hannu a shirin.

  • Shirin Gwamnati Na Samar Da Mafi Karancin Albashi
  • Wa’adin Da Gwamna Kano Ya Dauka Na Yi Wa Kwamishinoni Hisabi Ya Cika: Kila Wasu Za Su Karbi Littafinsu A Hannun Hagu

An kama jami’in jam’iyyar da ake zargi amma a ranar Talata, kuma ‘yan jam’iyyarsa sun ce “an kashe shi”.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin ta ce ta kama wasu da dama da suka kai harin, yayin da ake ci gaba da neman sauran amma kuma babu tabbas kan cewa an kama shugaban jam’iyyar, Yaya Dillo, amma a wani sako da ya wallafa a Facebook da safiyar Laraba, ya ce sojoji sun kewaye su.
Wannan na zuwa ne mako guda bayan da shugaban kotun kolin ya bayyana cewa an kai wa ofishinsa hari.

A halin yanzu jami’an tsaro na sintiri a titunan N’Djamena, yayin da al’ummar kasar suka shiga cikin fargaba.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

A wani ci gaban labarin kuma, a ranar 6 ga watan Mayu ne za a gudanar da zaben shugaban kasar Chadin wanda zai kawo karshen mulkin soji na shekaru uku da aka soma bayan shugaba Mahamat Idriss Deby Itno ya hau karagar mulki bayan rasuwar mahaifinsa a shekarar 2021.

Shugaban hukumar zaben kasar Ahmed Bartchiret, ya bayyana muhimman ranakun da za a gudanar da zaben shugaban kasar a lokacin da yake ganawa da manema labarai a Babban Birnin Kasar, N’Djamena, kamar yadda shafin intanet na Tchadinfos mai zaman kansa ya ruwaito.

Bartchiret ya jaddada muhimmancin gudanar da zaben kafin lokacin damina, inda ya bukaci abokan huldar fasaha da na kudi da su ba da hadin kai ga shirin zaben kasar.

Yayin da har yanzu shugaba Deby bai bayyana sake tsayawa takara ba a hukumance, ‘yan adawa sun bukaci da kada ya sake neman wani wa’adi.

Deby, mai shekaru 38, ya yi alkawarin shirya zabuka cikin watanni 18 bayan ya dare kan karagar mulki a watan Afrilun 2021.

Duk da haka, gwamnatinsa ta soji ta ci gaba da rike madafun iko, inda ta kara wa’adin mulkinta da karin watanni 18.

Chadi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Matasa Jami’An Sin Za Su Sauke Nauyin Ci Gaba Da Raya Tsarin Mulki Na Gurguzu Mai Sigar Musamman Ta Kasar

Matasa Jami’An Sin Za Su Sauke Nauyin Ci Gaba Da Raya Tsarin Mulki Na Gurguzu Mai Sigar Musamman Ta Kasar

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.