• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Za Ta Farfado Da Rukunin Gidaje Masu Saukin Kudi 46 A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Gidaje

Bankin da ke bayar da lamunin gina gidaje na kasa wato FMBN, ya kirkiro da aikin gyaran ayyukan gidajen da aka yi wasti da su kimanin 46 a daukacin fadin Nijeriya.

Domin bankin ya cimma wannan kudurin na sa, ya yi hadaka da bankin bunkasa Afrika na gina gidaje wato (ADB).

  • Bata Gari Sun Daka Wa Motar BUA Wawa A Kan Hanyar Zariya
  • An Fara Gudun Yada-kanin-wani A Gasar Firimiya

Bankin na ADB dai, ya kasance wata cibiyar bayar da daukin kudade ne da ke bayar da goyon baya wajen gina rukunin gidaje a Afrika.

Manajin Darakta na banin FMBN Shehu Usman Osidi ne ya bayyana hakan a kwanan baya a Abuja, lokacin da ya karbi bakuncin mahukutan bankin na ADB.

A caewar Shehu, bankin na FMBN na bayar da fifiko wajen sake farfado da rukunin gidaje da ke a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

Ya kara da cewa, bisa kara karfafa hadar zata taimaka wajen gina gidaje da kuma samar da rance ga masu gina rukunin gidaje a Nijeriya.

Shehu ya ci gaba da cewa, a Nijeriya a jihohi 36 akwai ayyukan gidaje sama da 46 da aka yi watsi da su, wadanda bankin na FMBN ya kudiri aniyar gyransu

Ya ci gaba da cewa,“Bincike ya nuna cewa, wasu bankuna sun kulla yarjajeniyar da jihohi yarjajeniyar domin bayar da kudade don gina gidaje, wanda ake sa ran jihohin za su samar da kayan aiki domin gina rukunin gidaje”.

Sai dai, Shehu ya ce, amma abun takaici akasarin jihohin sun gaza cika alkawuransu, wanda hakan ya janyo aka yi watsi da ayyukan na gina gidajen a jihohin su.

Shehu ya ce,“ Mun mun tuntubi bankin na ADB, wanda muka gano cewa, suna bayar da kudade, a saboda hana, mun shigo da su don su bayar da kudade don fara aikin farfado da ayyukan na gina gidajen don sayar da su ga ‘yan Nijeriya masu bukata”.

Ya kara da cewa, Nijeriya ce ta biyu da ke da hannun jari a bankin wanda ya kai kimanin kashi 15, wanda hakan zai bamu damar yin dubi kan yadda za a samar da kudade domin mu cimma burin mu na gina gidaje 100,000 ga ‘yan Nijeriya a 2024.

Ya ce, a yanzu bankin na FMBN na kan nazari kan yarjejeniyar da aka kaulla aka kuma yi watsi da ita kuma manufar ita ce domin amfanin ‘yan Nijeriya.

A na sa jawabin, shugaban bankin na ADB Thierno-Habib Hann ya ce, bankin na ADB ya zo Nijeriya ne wanzar da ajandarsa ta samar da kudaden bunkasa gidaje, wanda kuma ya gano cewa, Nijeriya masauki ce ta zuba jarin da ya kai sama da dala biliyan 25bn a duk shekara.

A cewarsa,“ A shirye muke mu yi hadaka da bankin FMBN da kuma sauran cibiyoyin da ke Nijeriya don mu cike gibin da ake da shi, na karancin gidaje, inda ya kara da cewa, kalubalem suna nan har da damar”.

A cikin wani kundin ta mika ragamar shugabanci da wakilinmu ya samu, tsohon Manajin Darakta na bankin FMBN Madu Hamman ya ce, shirin aikin gina giaje na NHF, bankin FMBN ne ya kirkiro da shi don ci gaba da gina gidaje a cikin saukin kudi ta hanyar zuba jari na dogon zango wanda za a rinka cire kashi 2.5, daga cikin albashin ma’aikata.

Madu ya kara da cewa, wasu daga cikin ci gaba da aka samu a watanni 12 da suka wuce a karo na farko a 2023, daukin kudaden da aka karbo sun dara Naira biliyan 100.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025
sallah
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
Next Post
Mutum 6 Sun Kamu Da Cutar Sanƙarau A Bauchi

Mutum 6 Sun Kamu Da Cutar Sanƙarau A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.