ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Za Ta Farfado Da Rukunin Gidaje Masu Saukin Kudi 46 A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Gidaje

Bankin da ke bayar da lamunin gina gidaje na kasa wato FMBN, ya kirkiro da aikin gyaran ayyukan gidajen da aka yi wasti da su kimanin 46 a daukacin fadin Nijeriya.

Domin bankin ya cimma wannan kudurin na sa, ya yi hadaka da bankin bunkasa Afrika na gina gidaje wato (ADB).

  • Bata Gari Sun Daka Wa Motar BUA Wawa A Kan Hanyar Zariya
  • An Fara Gudun Yada-kanin-wani A Gasar Firimiya

Bankin na ADB dai, ya kasance wata cibiyar bayar da daukin kudade ne da ke bayar da goyon baya wajen gina rukunin gidaje a Afrika.

ADVERTISEMENT

Manajin Darakta na banin FMBN Shehu Usman Osidi ne ya bayyana hakan a kwanan baya a Abuja, lokacin da ya karbi bakuncin mahukutan bankin na ADB.

A caewar Shehu, bankin na FMBN na bayar da fifiko wajen sake farfado da rukunin gidaje da ke a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Ya kara da cewa, bisa kara karfafa hadar zata taimaka wajen gina gidaje da kuma samar da rance ga masu gina rukunin gidaje a Nijeriya.

Shehu ya ci gaba da cewa, a Nijeriya a jihohi 36 akwai ayyukan gidaje sama da 46 da aka yi watsi da su, wadanda bankin na FMBN ya kudiri aniyar gyransu

Ya ci gaba da cewa,“Bincike ya nuna cewa, wasu bankuna sun kulla yarjajeniyar da jihohi yarjajeniyar domin bayar da kudade don gina gidaje, wanda ake sa ran jihohin za su samar da kayan aiki domin gina rukunin gidaje”.

Sai dai, Shehu ya ce, amma abun takaici akasarin jihohin sun gaza cika alkawuransu, wanda hakan ya janyo aka yi watsi da ayyukan na gina gidajen a jihohin su.

Shehu ya ce,“ Mun mun tuntubi bankin na ADB, wanda muka gano cewa, suna bayar da kudade, a saboda hana, mun shigo da su don su bayar da kudade don fara aikin farfado da ayyukan na gina gidajen don sayar da su ga ‘yan Nijeriya masu bukata”.

Ya kara da cewa, Nijeriya ce ta biyu da ke da hannun jari a bankin wanda ya kai kimanin kashi 15, wanda hakan zai bamu damar yin dubi kan yadda za a samar da kudade domin mu cimma burin mu na gina gidaje 100,000 ga ‘yan Nijeriya a 2024.

Ya ce, a yanzu bankin na FMBN na kan nazari kan yarjejeniyar da aka kaulla aka kuma yi watsi da ita kuma manufar ita ce domin amfanin ‘yan Nijeriya.

A na sa jawabin, shugaban bankin na ADB Thierno-Habib Hann ya ce, bankin na ADB ya zo Nijeriya ne wanzar da ajandarsa ta samar da kudaden bunkasa gidaje, wanda kuma ya gano cewa, Nijeriya masauki ce ta zuba jarin da ya kai sama da dala biliyan 25bn a duk shekara.

A cewarsa,“ A shirye muke mu yi hadaka da bankin FMBN da kuma sauran cibiyoyin da ke Nijeriya don mu cike gibin da ake da shi, na karancin gidaje, inda ya kara da cewa, kalubalem suna nan har da damar”.

A cikin wani kundin ta mika ragamar shugabanci da wakilinmu ya samu, tsohon Manajin Darakta na bankin FMBN Madu Hamman ya ce, shirin aikin gina giaje na NHF, bankin FMBN ne ya kirkiro da shi don ci gaba da gina gidaje a cikin saukin kudi ta hanyar zuba jari na dogon zango wanda za a rinka cire kashi 2.5, daga cikin albashin ma’aikata.

Madu ya kara da cewa, wasu daga cikin ci gaba da aka samu a watanni 12 da suka wuce a karo na farko a 2023, daukin kudaden da aka karbo sun dara Naira biliyan 100.

Gidaje
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Mutum 6 Sun Kamu Da Cutar Sanƙarau A Bauchi

Mutum 6 Sun Kamu Da Cutar Sanƙarau A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.