ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Za Ta Farfado Da Rukunin Gidaje Masu Saukin Kudi 46 A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Gidaje

Bankin da ke bayar da lamunin gina gidaje na kasa wato FMBN, ya kirkiro da aikin gyaran ayyukan gidajen da aka yi wasti da su kimanin 46 a daukacin fadin Nijeriya.

Domin bankin ya cimma wannan kudurin na sa, ya yi hadaka da bankin bunkasa Afrika na gina gidaje wato (ADB).

  • Bata Gari Sun Daka Wa Motar BUA Wawa A Kan Hanyar Zariya
  • An Fara Gudun Yada-kanin-wani A Gasar Firimiya

Bankin na ADB dai, ya kasance wata cibiyar bayar da daukin kudade ne da ke bayar da goyon baya wajen gina rukunin gidaje a Afrika.

ADVERTISEMENT

Manajin Darakta na banin FMBN Shehu Usman Osidi ne ya bayyana hakan a kwanan baya a Abuja, lokacin da ya karbi bakuncin mahukutan bankin na ADB.

A caewar Shehu, bankin na FMBN na bayar da fifiko wajen sake farfado da rukunin gidaje da ke a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Ya kara da cewa, bisa kara karfafa hadar zata taimaka wajen gina gidaje da kuma samar da rance ga masu gina rukunin gidaje a Nijeriya.

Shehu ya ci gaba da cewa, a Nijeriya a jihohi 36 akwai ayyukan gidaje sama da 46 da aka yi watsi da su, wadanda bankin na FMBN ya kudiri aniyar gyransu

Ya ci gaba da cewa,“Bincike ya nuna cewa, wasu bankuna sun kulla yarjajeniyar da jihohi yarjajeniyar domin bayar da kudade don gina gidaje, wanda ake sa ran jihohin za su samar da kayan aiki domin gina rukunin gidaje”.

Sai dai, Shehu ya ce, amma abun takaici akasarin jihohin sun gaza cika alkawuransu, wanda hakan ya janyo aka yi watsi da ayyukan na gina gidajen a jihohin su.

Shehu ya ce,“ Mun mun tuntubi bankin na ADB, wanda muka gano cewa, suna bayar da kudade, a saboda hana, mun shigo da su don su bayar da kudade don fara aikin farfado da ayyukan na gina gidajen don sayar da su ga ‘yan Nijeriya masu bukata”.

Ya kara da cewa, Nijeriya ce ta biyu da ke da hannun jari a bankin wanda ya kai kimanin kashi 15, wanda hakan zai bamu damar yin dubi kan yadda za a samar da kudade domin mu cimma burin mu na gina gidaje 100,000 ga ‘yan Nijeriya a 2024.

Ya ce, a yanzu bankin na FMBN na kan nazari kan yarjejeniyar da aka kaulla aka kuma yi watsi da ita kuma manufar ita ce domin amfanin ‘yan Nijeriya.

A na sa jawabin, shugaban bankin na ADB Thierno-Habib Hann ya ce, bankin na ADB ya zo Nijeriya ne wanzar da ajandarsa ta samar da kudaden bunkasa gidaje, wanda kuma ya gano cewa, Nijeriya masauki ce ta zuba jarin da ya kai sama da dala biliyan 25bn a duk shekara.

A cewarsa,“ A shirye muke mu yi hadaka da bankin FMBN da kuma sauran cibiyoyin da ke Nijeriya don mu cike gibin da ake da shi, na karancin gidaje, inda ya kara da cewa, kalubalem suna nan har da damar”.

A cikin wani kundin ta mika ragamar shugabanci da wakilinmu ya samu, tsohon Manajin Darakta na bankin FMBN Madu Hamman ya ce, shirin aikin gina giaje na NHF, bankin FMBN ne ya kirkiro da shi don ci gaba da gina gidaje a cikin saukin kudi ta hanyar zuba jari na dogon zango wanda za a rinka cire kashi 2.5, daga cikin albashin ma’aikata.

Madu ya kara da cewa, wasu daga cikin ci gaba da aka samu a watanni 12 da suka wuce a karo na farko a 2023, daukin kudaden da aka karbo sun dara Naira biliyan 100.

Gidaje
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Mutum 6 Sun Kamu Da Cutar Sanƙarau A Bauchi

Mutum 6 Sun Kamu Da Cutar Sanƙarau A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.