• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Ayyuka Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara Kan Ayyukan Sabunta Birane

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Ministan Ayyuka Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara Kan Ayyukan Sabunta Birane
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya samu yabo daga Ministan Ayyuka, David Umahi, bisa gagarumin ci gaban da gwamnatinsa ta samu a ayyukan sabunta birane.

A ranar Juma’ar ce Ministan ya kai ziyarar aiki Jihar Zamfara a wani rangadin da yake yi na duba ayyukan titunan Gwamnatin Tarayya a jihar.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce ministan ya duba ayyukan titunan Gwamnatin Tarayya da ke gudana wanda ya kai tsawon kilomita 277.305, daga Zariya zuwa Sheme, Sheme zuwa Gusau, da Gusau zuwa Mafara.

Sanarwar ta ƙara da cewa, ministan da muƙarrabansa sun lura da ɗumbin nasarorin da aka samu a aikin sabunta biranen da gwamnatin Gwamna Lawal ke gudanarwa.

  • Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

 

Labarai Masu Nasaba

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya yaba wa ministan bisa yunƙurinsa na duba ayyukan manyan titunan Gwamnatin Tarayya.

“Ina tabbatar muku da cewa akwai alheri domin akan bayar da kwangilar gina tituna, amma babu wanda ke zuwa dubawa daga Gwamnatin Tarayya. Zuwar ku na da matuƙar amfani..

“Minista, kamar yadda ka tabbatar, ba a daina faɗaɗa hanyoyi ba, kamar yadda ake ta yayatawa. Wannan labari ne mai daɗi.

“Ina so in nuna godiyata da kyawawan kalamanka. A matsayinmu na gwamnati mai kishin ƙasa, muna aiki tuƙuru don ganin mun canja mummunan yanayin Jihar Zamfara. A da, duk lokacin da ka ji labarin Jihar Zamfara, a kan yi tunanin abu mara kyau ne. Amma yanzu muna ƙoƙarin ceto da sake gina jihar.

“Ina kuma son in yi godiya ga shugaban ƙasa bisa ga ƙoƙarin da ya yi na aiwatar da muhimman ayyukan Gwamnatin Tarayya. Za mu ci gaba da goyon bayan kyawawan manufofinsa.”

A jawabinsa, ministan ayyuka, David Umahi, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne umarci a yi rangaɗin domin ganin yadda ayyukan ke gudana.

“Gwamna, mun zo nan ne bisa umarnin shugaban ƙasa domin duba ayyukan tituna da ke gudana tare da isar da gaisuwarsa gare ku.

“Shugaban ƙasa ya ƙuduri aniyar kammala dukkan ayyukan da ake gudanarwa, da suka haɗa da faɗaɗa titunan tarayya, ba a Zamfara kaɗai ba har ma a faɗin ƙasar nan baki ɗaya.

“Ina yaba muku kan ƙoƙorin ku na ci gaba da aiwatar da ayyukan sabunta birane da suka kawo sauyi a Zamfara cikin watanni tara kacal.”

Shugaban kwamitin Majalisar Dattijai mai kula da gidaje da tituna, Aminu Waziri Tambuwal, tsohon gwamnan Jihar Sakkwato yana cikin tawagar ministan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyyukaBiraneDauwa LawalMinistaTitunaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamitin Majalisa Zai Kammala Garanbawul Na Kundin Tsarin Mulki Cikin Wata 24

Next Post

Buhari Ya Haddasa Wa Nijeriya Koma-baya Na Tsawon Shekara 50 — Fayose

Related

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

12 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

12 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

13 hours ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

14 hours ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

16 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

18 hours ago
Next Post
Buhari Ya Haddasa Wa Nijeriya Koma-baya Na Tsawon Shekara 50 — Fayose

Buhari Ya Haddasa Wa Nijeriya Koma-baya Na Tsawon Shekara 50 — Fayose

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.