• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Fara Rubutu Don Daukaka Ko Neman Shahara Ba – Maimuna Tijjani

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
in Adabi
0
Ban Fara Rubutu Don Daukaka Ko Neman Shahara Ba – Maimuna Tijjani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Maimuna Tijjani Iyam na daya daga cikin marubutan littattafan Hausa a yanar gizo masu tasowa. A ttaunawarta da Wakiliyarmu Princess Fatima Zarah Mazadu ta bayyanawa masu karatu dalilin da ya sa ta fara rubutu har ma da bangaren da ta fi karkata wajen yin rubutun, har ma da wasu batutuwan masu yawa. Ga dai Yadda tattaunawar ta kasance:

Masu karatu za su so su ji cikakken sunanki?

Sunana Maimuna Tijjani Iyam

 

Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

Labarai Masu Nasaba

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

Da farko kamar yadda na fada sunana Maimuna Tijjani Iyam haifaffiyar jihar Yobe cikin karamar hukumar Potiskum, a nan nayi makaranta tun daga kan ‘Nursery School’ har yanzu da nake matakin kama da ‘Secondary’ ina karatu a ‘Federal College Of Education Potiskum’ ina karantar ‘Computer/Biology’.

 

Me ya ja hankalinki har ki ka fara rubutu?

Gaskiya tun ina karama na tashi da sha’awar rubutu da kuma karance-karance, tun ba iya rubutun hausa ba nake kwatanta rubuta labari ta hanyar zanen hoto har na iya, a takaice dai sha’awa da son ba wa al’ummata gudumawa shi ya ja hankali na tsunguma harkar rubutu.

 

Za ki shekara nawa da fara rubutu?

Na fara rubutu tun ina aji uku a ‘Primary’ tun lokacin hausar bata gama zauna mini dai-dai ba wajen rubutata a rubuce.

 

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

An sha gwagwarmaya amma yanzu Alhamdulillah, matsalar farko da na fara cin karo da ita shi ne kafin a amince mini a gida na fara rubutun kasancewar karancin shekaruna a lokacin.

 

Kina so ki ce iyayenki ba su amince da fara rubutunki ba?

Gaskiya an nuna rashin amincewa don cikin wasa na fara sanar da mahaifiyata amma sai ta nuna mini bata so, duk da ita ma ma’abociyar karance-karance sosai, sai daga baya kuma na samu amincewar su wanda yanzu Alhamdulillahi.

 

Kamar wanne bangare ki ka fi maida hankali akai wajen yin rubutu?

Na fi mai da hankali game da abubuwan da suke faruwa a rayuwar mu ta yau da kullum, kuma duk wanda ya karanta littafina ya san hakan, gaskiya ban fiye gina jigon labari cakocam akan soyayya ba.

Kin rubuta labari sun kai kamar guda nawa?

Labarai biyar gare ni daga lokacin da na fara zuwa yanzu daan lokacin dana fara ina rubutawa a takarda kafin na mallaki waya na rasa da yawa daga cikinsu.

 

Ya farkon farawarki ya kasance?

Gaskiya farkon fara rubutuna bai zo mini da wata matsala ba, kasancewar kafin na fara na zurfafa bincike sosai a harkar, har na tsinci wasu ilmin tun kafin na ma fara.

 

Wane labari ne ya fi baki wahala wajen rubutawa?

‘Matan Arewa’ Gaskiya shi ya fi bani wahala, domin rubutu ne mai fadi sosai da ya kunshi abubuwa da yawa musamman akan mata da irin rayuwar da suke fuskanta a arewa.

 

Kin taba buga labarinki?

A’a babu sai dai niyya.

 

Wanne irin nasarori ki ka samu game da rubutu?

Alhamdulillah na samu nasarori sosai musamman addu’o’in jama’a, na dauki hakan babban nasarar da kudi ba za su saya min su ba.

 

Ya ki ka dauki rubutu a wajenki?

Na dauki rubutu wata hanyar isar da sako ga jama’a mai cike da hikima.

 

Mene ne burinki na gaba game da rubutu?

Burina a rubutu shi ne sakon da nake son isarwa su kai inda kafafuna ko muryata basu da damar zuwa, domin ban fada harkar rubutu don zama sananniya ko kuma domin bidar shahara ba, illa iyaka son bada tawa gudumawar ga al’umma ta hanyar ruwan alkalamina.

 

Bayan rubutu kina wata sana’ar?

Eh! ina harkan ‘Graphics’.

 

Ya ki ke iya hada rubutunki da kuma sana’arki?

Kowanne da lokacinsa kuma babu wanda yake shiga lokacin wani.

 

Kamar da wanne lokaci ki ka fi jin dadin yin rubutu?

Safe da kuma yammaci don sam bana yin rubutu da rana.

 

Me za ki ce da masoyanki?

Babu abin da zance dasu face godiya na gode da soyayyarsu gare ni Allah ya bar zumunci da kauna tsakaninmu.

 

Ko kinada wadanda za ki gaisar?

Da farko iyayena Alh.Tijjani Iyam da kuma malama Aisha Ishak Fada, sai kuma Ahmad Toshiba wanda ya zamto tamkar dan uwan da muka fito ciki daya dashi wanda harkar rubutu ce ta hada mu, sai kuma ‘yan uwa da abokan arziki da makaranta littattafaina


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Kaddamar Da Taro Na Biyu Na Majalisar CPPCC Karo Na 14 Gobe Litinin

Next Post

Shugaban Kasar Saliyo Na Fatan Hadin Gwiwar Aikin Gona Da Lardin Hubei Na Kasar Sin 

Related

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

5 months ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

8 months ago
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya
Adabi

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

10 months ago
Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
Adabi

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

10 months ago
Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk
Adabi

Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk

10 months ago
Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
Adabi

Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad

12 months ago
Next Post
Shugaban Kasar Saliyo Na Fatan Hadin Gwiwar Aikin Gona Da Lardin Hubei Na Kasar Sin 

Shugaban Kasar Saliyo Na Fatan Hadin Gwiwar Aikin Gona Da Lardin Hubei Na Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.