• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ofishin Kwamitin Amintattu Na Asusun Tsaro

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ofishin Kwamitin Amintattu Na Asusun Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Zamfara, ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal, ta ƙaddamar da ofishin amintattun Asusun Kula da Harkokin Tsaro domin daƙile ayyukan ’yan bindiga da sauran ta’addanci a jihar, inda Gwamnan ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tallafa wa asusun ta kowane fanni.

A ranar Juma’ar Gwamna Lawal ya jagoranci ƙaddamar da ginin amintattun Asusun Kula da Harkokin Tsaro da ke Gusau babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce asusun tsaron na Zamfara yana ƙarƙashin jagorancin Tsohon Sufeto Janar na ’yan sanda, MD Abubakar ne.

  • Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

 

A cewar sanarwar, an ƙaddamar da aikin ne a ƙarƙashin wani kwamitin amintattu na ƙwararru a fannin tsaro domin aiwatar da aikin yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

A yayin bikin ƙaddamar da ginin, Gwamna Lawal ya buƙaci sauran jihohin ƙasar nan da su kafa irin waɗannan asusun amintattu, da daidaita tsare-tsare, da samar da tsarin da ya shafi tsaron yankin.

Ya ce, “Yayin da Asusun Tallafa wa Tsaro ya fara aiki cikin tsari, ina roƙon a haɗa hannu da irin waɗannan asusu da wasu jihohi ke kafawa a yankunan su domin haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen daƙile matsalar tsaro.

“Asusun yana da abubuwa da yawa da zai yi yayin da ya fara aiki. Wani abin da asusun zai ƙara mayar da hankali a kai shi ne tabbatar da cire wa yaranmu da matasanmu tunanin rikice-rikice da kuma nuna ƙabilanci, wanda hakan ke haifar da tayar da ƙayar baya a wasu al’ummomi. Wannan ya zama dole don samun ci gaba mai ma’ana kuma mai ɗorewa.

“A ƙarƙashin jagoranci mai nagarta na Shugaban Asusun, IGP M.D Abubakar (Mai Ritaya) da sauran jiga-jigan kwamitin amintattun, muna sa ido ga haɗin kanku don haɓaka rayuwar jama’armu nan take.

“Mun dogara da ku, domin mun san ku duka kuna da cancantar ɗaukar irin wannan nauyi. Na gode da hidimar ku da aikin ku ga jihar ku.

“Abin da ke faɗo min rai a duk lokacin da aka kai wani hari, shi ne yabo bisa ƙoƙarin da Rundunar Kare Jama’a ta Zamfara, wacce muka ƙaddamar kwanan nan take yi wajen ceto al’umma.

“Muna da niyyar ci gaba da ƙoƙari wajen haɗa kan al’umma, ci gaba da wayar da kan jama’a, da kuma tabbatar da bin ƙa’idojin aiki da dukkan mambobin Rundunar Kare Jama’a ta Zamfara suka rantse a kai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GiniJihar ZamfaraOfishiTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sakataren Tsaron Amurka Ya Amince Da Samun “Kudin Yaki” A Fili

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yammata Masu Yawon Dare A Yamai

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

9 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

9 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

11 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

12 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

14 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke ‘Yammata Masu Yawon Dare A Yamai

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yammata Masu Yawon Dare A Yamai

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.