• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS: ACG James Sunday Ya Kai Ziyarar Inganta Aiki Maiduguri

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
NIS: ACG James Sunday Ya Kai Ziyarar Inganta Aiki Maiduguri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS), ACG James Sunday, ya ziyarci kwamandan rundunar Operation Hadin Kai a hedikwatar hukumar da ke Arewa maso Gabas a Maiduguri a karkashin jagorancin Manjo Janar W Shaibu domin tattauna gudunmawar da hukumar za ta bai wa rundunar a Maiduguri.

Taron ya samu halartar Babban Kwanturolan hukumar reshen Jihar Borno, CIS Abba Salihu da mataimakansa da ke shiyyar C, Manjo Janar W Shaibu da sauran manyan hafsoshin soji da ke hadin gwiwa da rundunar.

  • Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman
  • Abubuwan Da Za Su Taimaka Wa Mai Azumi Ya Kasance Cikin Koshin Lafiya

Ko’odinetan Shiyyar C (Arewa maso Gabas), wadda ta kunshi jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Yobe da Filato bayan sun ziyarci jihar Yobe, ya ziyarce su ne domin tantance ayyukan rundunar tare da jadadda umarnin sake bude iyakar Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, sannan zai dawo Maiduguri domin ci gaba da ziyarar aikin kwanaki biyu a jihohin Borno da Yobe.

Haka zalika hukumar ta umarci rundundar da ke Jihar Borno da ta sake bude iyakar Nijeriya ci gaba da zirga-zirgar mutane zuwa Nijeriya da da sauran al’amuran yau da kullum kamar da yadda aka saba a baya.

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa tana da jami’ai da maza kusan 230 da aka tura zuwa rundunar hadin gwiwa, domin kyautata dangantakar ta aiki da hadin kai.

Labarai Masu Nasaba

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

A cewar Kwamandan, jami’an NIS sun kware sosai wajen aikinsu dangane da shige da fice da sauransu. Jami’an sun samu horo da tsarin aiki karkashin jagorancin Manjo Janar W Shaibu kamar yadda aka bayyana a yayin taron.

“Ni da kaina na taso daga Maiduguri zuwa Damaturu domin tantance yanayin aikin da ake yi”, in ji ACG James.

“Ina tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa an samu kwanciyar hankali da tsaro a yankin Arewa maso Gabas, harkokin tattalin arziki da na cikin gida sun dawo a jihohin Barno da Yobe, motoci suna zirga-zirga cikin lafiya tare da kayayyaki zuwa sassan kasar nan.

“Ina mika godiya ga dukkan jami’an da ke kan hanyar da sojoji ke aiki ba dare ba rana a kewayen tafkin Chadi da kan iyaka, wannan namijin kokari ne kuma abun a yaba ne, in ji shi.

“Ina son jinjina wa jami’ain NIS tare da mika godiyata a gare su.”

Gwamnatin Jihar Borno ta za ta shirya wani babban taron tsaro a Maiduguri, bisa tsarin NIS a yankin Arewa Maso Gabas, don samar da hanyoyin da za a tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin a kamar yadda mataimakin gwamnan jihar, Umar Usman Kadafur ya bayyana a lokacin da ya ziyarci ofishin hukumar na shiyyar C, da ke gidan gwamnatin jihar a Maiduguri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman

Next Post

Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

Related

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
Labarai

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

2 hours ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

8 hours ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

9 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
Labarai

An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi

11 hours ago
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

13 hours ago
Next Post
Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

LABARAI MASU NASABA

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

May 30, 2025
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

May 30, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

May 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

May 30, 2025
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.