• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS: ACG James Sunday Ya Kai Ziyarar Inganta Aiki Maiduguri

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
NIS: ACG James Sunday Ya Kai Ziyarar Inganta Aiki Maiduguri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS), ACG James Sunday, ya ziyarci kwamandan rundunar Operation Hadin Kai a hedikwatar hukumar da ke Arewa maso Gabas a Maiduguri a karkashin jagorancin Manjo Janar W Shaibu domin tattauna gudunmawar da hukumar za ta bai wa rundunar a Maiduguri.

Taron ya samu halartar Babban Kwanturolan hukumar reshen Jihar Borno, CIS Abba Salihu da mataimakansa da ke shiyyar C, Manjo Janar W Shaibu da sauran manyan hafsoshin soji da ke hadin gwiwa da rundunar.

  • Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman
  • Abubuwan Da Za Su Taimaka Wa Mai Azumi Ya Kasance Cikin Koshin Lafiya

Ko’odinetan Shiyyar C (Arewa maso Gabas), wadda ta kunshi jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Yobe da Filato bayan sun ziyarci jihar Yobe, ya ziyarce su ne domin tantance ayyukan rundunar tare da jadadda umarnin sake bude iyakar Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, sannan zai dawo Maiduguri domin ci gaba da ziyarar aikin kwanaki biyu a jihohin Borno da Yobe.

Haka zalika hukumar ta umarci rundundar da ke Jihar Borno da ta sake bude iyakar Nijeriya ci gaba da zirga-zirgar mutane zuwa Nijeriya da da sauran al’amuran yau da kullum kamar da yadda aka saba a baya.

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa tana da jami’ai da maza kusan 230 da aka tura zuwa rundunar hadin gwiwa, domin kyautata dangantakar ta aiki da hadin kai.

Labarai Masu Nasaba

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

A cewar Kwamandan, jami’an NIS sun kware sosai wajen aikinsu dangane da shige da fice da sauransu. Jami’an sun samu horo da tsarin aiki karkashin jagorancin Manjo Janar W Shaibu kamar yadda aka bayyana a yayin taron.

“Ni da kaina na taso daga Maiduguri zuwa Damaturu domin tantance yanayin aikin da ake yi”, in ji ACG James.

“Ina tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa an samu kwanciyar hankali da tsaro a yankin Arewa maso Gabas, harkokin tattalin arziki da na cikin gida sun dawo a jihohin Barno da Yobe, motoci suna zirga-zirga cikin lafiya tare da kayayyaki zuwa sassan kasar nan.

“Ina mika godiya ga dukkan jami’an da ke kan hanyar da sojoji ke aiki ba dare ba rana a kewayen tafkin Chadi da kan iyaka, wannan namijin kokari ne kuma abun a yaba ne, in ji shi.

“Ina son jinjina wa jami’ain NIS tare da mika godiyata a gare su.”

Gwamnatin Jihar Borno ta za ta shirya wani babban taron tsaro a Maiduguri, bisa tsarin NIS a yankin Arewa Maso Gabas, don samar da hanyoyin da za a tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin a kamar yadda mataimakin gwamnan jihar, Umar Usman Kadafur ya bayyana a lokacin da ya ziyarci ofishin hukumar na shiyyar C, da ke gidan gwamnatin jihar a Maiduguri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman

Next Post

Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

Related

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

11 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

13 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

15 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

17 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

19 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

19 hours ago
Next Post
Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

LABARAI MASU NASABA

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.