• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lauyoyi Mata Sun Koka Kan Cin Zarafin Da Alkalai Maza Ke Yi Musu A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Lauyoyi Mata Sun Koka Kan Cin Zarafin Da Alkalai Maza Ke Yi Musu A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar lauyoyi Mata ta kasa (NBA) reshen jihar Adamawa, ta koka da halayyar wasu alkalai da jami’an ma’aikatan kotu a jihar kan cin zarafin mambobin kungiyar.

Duk da dai matan ba su fadi irin cin zarafin da mazan alkalan ke musu ba, amma tuni kungiyar ta kai kara ga babbar alkalin alkalai ta jihar , Mai shari’a Hafsat Abdulrahaman, ta kuma bukaci Mai shari’ar da ta gudanar da bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda aka samu da laifi.

  • PCRC Ta Zabi Sabbin Shugabanni A Adamawa
  • Gwamna Fintiri Ya Maka Dakataccen Kwamishinan INEC Na Adamawa, Hudu Ari A Kotu

Barista Fatima Raji Bello, ita ce shugabar Kungiyar Mata Lauyoyi ta Jihar, ta bayyana haka lokacin da su ka kai ziyarar goyon baya ga babbar mai shari’ar, Hafsat Abdulrrahaman, domin tunawa da ranar mata ta duniya a jihar.

Ta ce tuni “Kungiyar ta gabatar da koken cin zarafin da wasu alkalai mazan da jami’an kotuna ga ofsin babbar mai shari’ar.

“Muna kuma bukatar da ku binciki zargin domin ku hukunta duk wadanda ke da hannu a ciki, Muna kira da a horar da dukkan ma’aikatan shari’a kan keta ka’idojin lalata da cin zarafin mata” inji Raji.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

Haka kuma shugabar kungiyar ta shaidawa Mai shari’a Hafsat, cewa sun kuma kawo mata ziyarar ne domin jin ta bakinta game da ayyukan da su ka fara a shekarar 2022, sannan ta bukace ta a matsayin uwar Lauya da Bench da su shiga kungiyar ta NBA domin ba su horo da matasa da masu neman zama lauyoyi mata a harkar sana’a a jihar.

Ta kuma yi amfani da ziyarar wajen yabawa babban mai shari’a, Hafsat AbdulRahman da kwamishinan shari’a da kuma babban lauyan gwamnatin jihar, Barista Jingi Afraimu, da ya dauki nauyin lauyoyi 14 domin halartar taro na 2, 3 da 4 na kungiyar matan NBA da aka gudanar a jihar Legas da Abuja.

Da take mayar da martani, babbar mai shari’a, Hafsat Abdulrahaman, ta bayar da hakuri ga duk wani nau’in cin zarafin da alkalai ke yi wa mata lauyoyin, sannan ta yi alkawarin tabbatar da gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Ta kuma nuna jin dadi da yadda mata ke samun gagarumin tasiri a kowane fanni na al’amura da sana’o’in da su ka sa a gaba, ta kuma yaba wa alkalai mata musamman wajen yin tasiri sosai kan hukunce-hukunce, tare da bayyana kyakkyawan fata na cewa dandalin Mata lauyoyin zai iya yin abin da ya dace wajen tallafa wa juna.

Mai shari’ar ta kuma yaba tare da godewa shugabanni da mambobin kungiyar bisa wannan ziyara, inda ta bukace su da su kara himma domin aikin lauya ya na bukatar a kula da da’a, kwazon, aiki tukuru da kuma tsafta da ado.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaLauyoyi MataMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Sanata Yari Ya Buƙaci Musulmi Da Su Yi Wa Shugaba Tinubu Addu’a

Next Post

Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

1 hour ago
Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna
Labarai

Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

2 hours ago
Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 
Manyan Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

3 hours ago
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho
Manyan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

4 hours ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

4 hours ago
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000
Manyan Labarai

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

6 hours ago
Next Post
Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

LABARAI MASU NASABA

AC Milan Ta Amince Da Biyan Yuro Miliyan 36 Domin Daukar Nkunku Daga Chelsea

AC Milan Ta Amince Da Biyan Yuro Miliyan 36 Domin Daukar Nkunku Daga Chelsea

August 28, 2025
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Shigo Da Su Daga Kasashe Masu Karancin Ci Gaba Na Afrika Ya Karu Da Kaso 10.2 Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Shigo Da Su Daga Kasashe Masu Karancin Ci Gaba Na Afrika Ya Karu Da Kaso 10.2 Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

August 28, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

August 28, 2025
Shugabannin Kasashe 26 Za Su Halarci Bikin Ranar Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa A Ran 3 Ga Satumba

Shugabannin Kasashe 26 Za Su Halarci Bikin Ranar Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa A Ran 3 Ga Satumba

August 28, 2025
Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

August 28, 2025
Jimillar Kudaden Jigilar Kayayyaki a Watanni 7 Na Farkon Bana a Sin Ta Zarce Rmb Yuan Tiriliyan 200

Jimillar Kudaden Jigilar Kayayyaki a Watanni 7 Na Farkon Bana a Sin Ta Zarce Rmb Yuan Tiriliyan 200

August 28, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

August 28, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

August 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

August 28, 2025
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

August 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.