ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lauyoyi Mata Sun Koka Kan Cin Zarafin Da Alkalai Maza Ke Yi Musu A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Adamawa

Kungiyar lauyoyi Mata ta kasa (NBA) reshen jihar Adamawa, ta koka da halayyar wasu alkalai da jami’an ma’aikatan kotu a jihar kan cin zarafin mambobin kungiyar.

Duk da dai matan ba su fadi irin cin zarafin da mazan alkalan ke musu ba, amma tuni kungiyar ta kai kara ga babbar alkalin alkalai ta jihar , Mai shari’a Hafsat Abdulrahaman, ta kuma bukaci Mai shari’ar da ta gudanar da bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda aka samu da laifi.

  • PCRC Ta Zabi Sabbin Shugabanni A Adamawa
  • Gwamna Fintiri Ya Maka Dakataccen Kwamishinan INEC Na Adamawa, Hudu Ari A Kotu

Barista Fatima Raji Bello, ita ce shugabar Kungiyar Mata Lauyoyi ta Jihar, ta bayyana haka lokacin da su ka kai ziyarar goyon baya ga babbar mai shari’ar, Hafsat Abdulrrahaman, domin tunawa da ranar mata ta duniya a jihar.

ADVERTISEMENT

Ta ce tuni “Kungiyar ta gabatar da koken cin zarafin da wasu alkalai mazan da jami’an kotuna ga ofsin babbar mai shari’ar.

“Muna kuma bukatar da ku binciki zargin domin ku hukunta duk wadanda ke da hannu a ciki, Muna kira da a horar da dukkan ma’aikatan shari’a kan keta ka’idojin lalata da cin zarafin mata” inji Raji.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Haka kuma shugabar kungiyar ta shaidawa Mai shari’a Hafsat, cewa sun kuma kawo mata ziyarar ne domin jin ta bakinta game da ayyukan da su ka fara a shekarar 2022, sannan ta bukace ta a matsayin uwar Lauya da Bench da su shiga kungiyar ta NBA domin ba su horo da matasa da masu neman zama lauyoyi mata a harkar sana’a a jihar.

Ta kuma yi amfani da ziyarar wajen yabawa babban mai shari’a, Hafsat AbdulRahman da kwamishinan shari’a da kuma babban lauyan gwamnatin jihar, Barista Jingi Afraimu, da ya dauki nauyin lauyoyi 14 domin halartar taro na 2, 3 da 4 na kungiyar matan NBA da aka gudanar a jihar Legas da Abuja.

Da take mayar da martani, babbar mai shari’a, Hafsat Abdulrahaman, ta bayar da hakuri ga duk wani nau’in cin zarafin da alkalai ke yi wa mata lauyoyin, sannan ta yi alkawarin tabbatar da gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Ta kuma nuna jin dadi da yadda mata ke samun gagarumin tasiri a kowane fanni na al’amura da sana’o’in da su ka sa a gaba, ta kuma yaba wa alkalai mata musamman wajen yin tasiri sosai kan hukunce-hukunce, tare da bayyana kyakkyawan fata na cewa dandalin Mata lauyoyin zai iya yin abin da ya dace wajen tallafa wa juna.

Mai shari’ar ta kuma yaba tare da godewa shugabanni da mambobin kungiyar bisa wannan ziyara, inda ta bukace su da su kara himma domin aikin lauya ya na bukatar a kula da da’a, kwazon, aiki tukuru da kuma tsafta da ado.

Adamawa
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.