• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman Gwanda Da Kasuwancinta A Saukake

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Noman Gwanda Da Kasuwancinta A Saukake
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Ana samun dimbin kudin shiga a noman Gwanda a Nijeriya, amma babban abin taikaici shi ne, da yawan mutane ba su damu da yin nomanta ba.

Wasu masana a fannin, sun danganta rashin rugumar wannan fanni a kan rashin wayar musu da kai dangane da amfanin da ke tattare da noman na Gwanda.

  • An Fara Taron Kasa Da Kasa Kan Tsarin Dimokuradiyya Karo Na Uku A Nan Birnin Beijing
  • Yadda Kungiyar SSANU Da NASU Suka Gudanar Da Zanga-zangar Lumana A Zariya

Yadda Ake Renon Irin Gwanda:

Mataki na farko a noman Gwanda shi ne,  fara renon Irin da za a shuka na Gwandar.

Ka Tabbata Ka Sayo Ingantaccen Irin Da Za Ka Shuka:

Ka samu wajen da ya fi dacewa ka gyara tare da kone sharar da ke wajen, sai ka shuka Irin mita biyar tsakanin kowanne Iri haka, yana kai wa kimanin satuttuka kafin ya fara nuna ko kuma fiye da haka.

Bayan watanni biyu da shukawa, sai a nome ciyawar da ke gurin; sannan ka da kuma a zubar da ciyawar a bar ta a nan ta rube yadda za ta zama takin gargajiya.

Bayan wata daya zuwa biyu, sai a  canza mata waje; inda ake ganin zai fi gibin sama da mita biyar, bayan wata uku sai a sayo maganin feshi a yi wa kasar, wanda hakan zai sanya ta yin saurin girma.

Har ila yau, bayan wata shida sai a kara yin wani feshin, inda a cikin sati uku masu zuwa kacal za ta kara yin kyau, sai a bar ta zuwa wata uku ko fiye da haka, domin ta kara yin karfi.

Kasar Noman Da Ta Fi Dacewa:

Ka tabbatar da ka yi shuka a kasar noman da ta fi dacewa,  musammn don ka samu amfanin mai yawa,  haka nan ana so a yi shuka a kasar noman da ke da lema sosai.

Matakan Shuka Gwanda:

A wannan matakin, ana bukatar a ciro ta daga wadanda suka fara fitowa daga cikin abin da aka shuka Irin tun farko, sai a haka rami a shuka ta.

Lokacin  Da  Ya Fi Dacewa A  Shuka Ta:

Babu takamaiman lokacin da aka kebe na shuka ta, donin a kowane lokaci na kakar noma; za iya yin nomanta, har ila yau kuma ta na jure wa kowane irin yanayi.

Kwana Nawa Take Yi Kafin Ta Fara ‘Ya’ya?

Ya danganta da ingantaccen Irin da aka shuka da kuma yadda nau’in Gwandar yake, wasu na kai wa tsawon shekara hudu kafin su girma; tun daga lokcin da aka shuka Irin, haka nan kuma wasu na kai wa tsawon shekara takwas kafin su girma.

Lokacin Girbin Gwanda:

Yayin da jikinta ya fara canzawa zuwa yalo, sai dai wasu nau’in Gwandar, ba ya canzawa zuwa yalo idan sun nuna suna kuma kai wa wata tara bayan an canza wa Irin matsuguni daga inda aka dasa shi.

Bishiya daya ta Gwanda, za a iya samar da kimanin Gwanda daga 75 zuwa 100 a shekara, sannan ta na iya kaiwa tsawon shekaru dari ana cire ‘ya’yanta, amma an fi fara samun amfaninta daga shekaru uku zuwa hudu.

Kasuwancin Gwanda:

A yayin da ake jira ta kammala girma, sai a fara tuntubar masu bukatar saye ko kuma kasuwar da za a kai don sayarwa, haka nan za a iya tuntubar kamfanoni, musamman wadanda ke sarrafa ta zuwa wasu nau’ukan kayan lemon Kwalba, sarrafa magunguna da sauran makamantansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Nasarar Gudanar Da Dandalin Jihar Legas

Next Post

Takaitaccen Nazari A Kan Yadda Ake Noman Karas A Nijeriya

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

4 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

4 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

4 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Takaitaccen Nazari A Kan Yadda Ake Noman Karas A Nijeriya

Takaitaccen Nazari A Kan Yadda Ake Noman Karas A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.