ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaitaccen Nazari A Kan Yadda Ake Noman Karas A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Karas

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ko shakka babu, ana yin noman Karas yadda ya kamata a Nijeriya, sannan ya kasance kayan lambu na biyu a duniya da aka sani baya ga Dankali, kazalika kuma yana daukar daga kimanin kwana 70 zuwa 80 kafin ya fara nuna.

Haka zalika, Jihar Filato ce a kan gaba wajen nomansa a duk fadin wannan kasa, sakamakon yanayi da jihar ke da shi mai matukar kyau wanda ya da ce da nomansa.

  • Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma
  • Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

Yadda Ake Nomawa

Ana samun nau’ikan Irinsa da dama a Nijeriya, wadanda suke samar da amfanin gona mai tarin yawa, wasu daga cikin nau’ikan Irin da ake kira a turance sun hada da ‘Danbers, Chantanay, Nantes, Armsterdam’ da sauran makamantansu, wadanda kuma sun kasance suna bukatar ingattaciyar kasar noma.

Ganin cewa, Irinsa na da wuyar sha’ani yana kuma son kulawar da ta dace, ya zama wajibi a gyara gonar don shuka Irin yadda ya dace, haka nan; ya fi dacewa a shuka Irin a kan Kunyoyi yadda jijiyoyinsa za su samu sukunin shiga cikin kasar da aka shuka shi.

Amfanin Karas:

Yana da matukar amfani sosai ga rayuwar Dan Adam, domin kuwa ana yin amfani da shi wajen hada miya ko abinci tare da sarrafa shi zuwa kayan zaki, haka nan yana dauke da wasu sinadaran hada magunguna  da suka hada da ‘thiamine da riboflabin’.

Har ila ya, cin sa tsura na taimakawa wajen kara lafiyar jikin  dan Adam tare da da dai-daita sinadarin ‘cholesterol’ da ke rage kiba a jikin mutum.

Bugu da kari, yana dauke da sinadarin ‘beta carotene, bitamins A, D, C, E, K, potassium da kuma minerals’, wadanda suke taimaka wa wajen karin gani na Ido tare da kara gyara fatar jiki.

Har ila yau, Karas na dauke da sauran sinadaran da ke kara wa Dan Adam karfin jiki da wadanda suka hada da: ‘fat, protein, carbohydrates, sodium, zinc, phosphorus, potassium, manganese, calcium and iron’.

Yawan ruwan da ke jikinsa, ya kan kai  kashi 88 a cikin 100, wanda yake dauke da sindarin ‘protein da ya kai kimanin kashi 0.9 a cikin dari, sai kuma sinadarin ‘fibre’ da ya kai kashi 2.8 a cikin dari, inda sinadarin ‘fat’ ke dauke da kashi 0.2 a cikin dari, sai kuma sinadarin ‘carbohydrates’ da kashi 9 cikin dari.

Canjin Yanayi:

Karas ya fi son yanayi mai sanyi, musamman wanda ya kai  ma’unin yanayi daga 16 zuwa 20, amma ma’aunin yanayin da ya wuce 28, na rage masa saurin girma kuma idan aka shuka Irin yana kaiwa daga kimanin kwana bakwai zuwa 21 kafin ya fara fitowa daga cikin kasa.

Yadda Ake Shuka Shi:

Bayan an tona kasa an zuba Irin a yayin shuka shi, ana rufe shi ne a hankali, kazalika wasu manoman kan yi wa gonar da za su shuka shi ban ruwa har zuwa tsawon awa ashirin da hudu kafin su shuka Irin, musamman don ya samu danshi sosai. Sannan, ana kuma bukatar manomi ya nemi shawarar masana a kan wannan Iri da kuma Takin da ya dace ya yi amfani da shi.

Har ila yau, za a iya zuba Takin Gargajiya; bayan wata guda da shuka shi, domin amfanin ya yi saurin girma.

Ban Ruwa:

Karas na bukatar yawan ruwa, musamman a lokacin noman rani, don ya girma da wuri; kana kuma ana so bayan an shuka shi a tabbatar da an yi masa ban ruwa, domin ya kasance yana dauke da danshi.

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Da Girbin Karas:

Ana girbe shi ne, bayan an tabbatar da cewa ya gama girma yadda ya kamata, sannan manomi zai iya barin sa a gona ba tare da ya girbe shi ba, sai dai kuma ana bayar da shawara cewa; ka da a bar shi ya jima a inda aka shuka shi  ba tare da an girbe shi ba, don gudun ka da ya yi tauri. Haka nan, ana  girbe shi ne bayan jijiyarsa ta kai girman kimanin mita 1.8 ko kuma fiye da haka.

Ribar Nawa Manomi Yake Samu?

Bisa binceken da aka yi a kwanakin baya na tsadar farashin noman Karas, an kiyasta cewa kowace kadada daya; ta kai kimanin dala 10,600.

Nawa Ake Kashewa Wajen Noman Karas A Kadada Daya?

Kudaden da ake kashewa ciki har da na hayar gona a kowace Kadada daya, sun kai kimanin dala 4,200 zuwa dala 5,000, inda kuma sarrafa shi a kadada daya ya doshi daga dala 1,500 zuwa dala 2,000

Karas
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

Gwamnati Ta Bankado Sunaye 15 Da Ake Zargi Da Hannu A Tallafa Wa Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.