• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Na Sa Dokar Ta-ɓaci A Sashen Ilimin Jihar Zamfara – Gwamna Dauda Lawal

by Leadership Hausa
1 year ago
in Ilimi
0
Abin Da Ya Sa Na Sa Dokar Ta-ɓaci A Sashen Ilimin Jihar Zamfara – Gwamna Dauda Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa koma-bayan da aka samu a harkar ilimin jihar a baya ta sa ya ayyana dokar ta-ɓaci a sashen.

Ya kuma nunar da cewa ilimi wani ginshiƙi ne mafi muhimmanci ga ci gaban jihar Zamfara.

A Larabar nan ne ɗaliban makarantar ‘Leadsprings International Schools’ suka karrama Gwamna Lawal a gidan gwamnati da ke Gusau.

Kamar yadda yake ƙunshe a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Gusau, ya bayyana cewa waɗannan yara sun kuma miƙa wa Gwamnan wasu buƙatu guda bakwai masu muhimmanci, waɗanda su ke sa ran cimma a nan gaba.

Malam Idirs Bala ya ce, waɗannan tsammani da ake son cimma a aƙibar Zamfara, sun haɗa da babban birnin jihar, Gusau; sashen kiwon lafiya; harkar jiragen sama na Zamfara; fasaha; noma da sashen tattalin arziki, masana’antu da kamfanoni.

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

Cikin jawabin da ya yi wa waɗannan yara, Gwamna Dauda ya ƙara jaddada aniyarsa ta yin garambawul a harkar ilimi a jihar.

Gwamnan ya ce, “Ilimi ne abu na ɗaya cikin muhimman abubuwan da gwamnatina ta sanya a gaba, na biyu kuma, shi ne harkar tsaro. Sai dai harkar ilimin mu ba ta tafiya yadda ya kamata a lokutan baya. A kowane lokaci jihar Zamfara tana zamowa ta ƙarshe a harkar ilimi, wannan ne ya sa na sanya dokar ta-ɓaci a harkar ilimin.

zamfara

“Matakan sun haɗa da ɗaukar ƙwararrun Malaman da suka cancanta, samar da gine-gine da isassun kayan aiki, tare kuma da samar da hanyoyin koyarwa irin na zamani.

“Gwamnatina ba za ta gajiya ba, wajen sake fasalin harkar ilimi, ta yadda zai biya buƙatun al’ummarmu.

Daga nan kuma sai Gwamnan ya nuna jin daɗin sa bisa irin misalin ingantaccen ilimin da yaran suka nuna masa sun samu a makaranar tasu. Ya kuma gode wa Hukumar wannan makaranta ta ‘Leadsprings International School’ bisa wannan karramawa da suka yi masa.

zamfara

“Na ji daɗi da ganin irin yanayin karatunku da kuka nuna mana, wannan ya na nuni da cewa ɗaliban makarantar ‘Leadsprings International School’ a shirye suke su goga kafaɗa da kowa a faɗin duniyar nan.

“Ina godiya da wannan karramawa. Gwamnati na za ta ƙarfafa maku a duk inda za ta iya. Ina kira ga sauran makarantu masu zaman kansu su kwaikwayi wannan kyakkyawan aiki na ku.

Cikin nasa jawabin sa, mai makarantar ‘Leadsprings International School, Danjuma Sule ya bayyana cewa makarantarsa a shirye ta ke ta tafi da tsarin ilimin gwamnatin jihar Zamfara.

“Muna jinjina ga gwamnatin ka bisa irin jajircewarta wajen samar da yanayin karatu mai kyau a duk faɗin jihar. Muna kuma godiya da aniyar ka ta ɗaukaka ilimin mata a jihar. Yanzu haka, makarantar ‘Leadsprings International Schools’ muna da ɗalibai mata 386 a ajujuwa daban-daban, kuma muna nan muna nuna masu hanyoyin da za su zama masu amfani ga ci gaban Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna Dauda LawalHutun KaratuIlimiMakarantaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Hadin Gwiwa A Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Na MDD

Next Post

“Tutar Dimokuradiyya” Da Kasar Amurka Ta Rike Ta Lalace

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

19 hours ago
Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima
Ilimi

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

1 week ago
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Ilimi

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

3 weeks ago
Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya
Ilimi

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

3 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

4 weeks ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

1 month ago
Next Post
Amurka

"Tutar Dimokuradiyya" Da Kasar Amurka Ta Rike Ta Lalace

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.