• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hasashe A Kan Sabon Yunkurin el-Rufai Da Zargin Ficewarsa APC

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Hasashe A Kan Sabon Yunkurin el-Rufai Da Zargin Ficewarsa APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan nan, hankula sun karkata a kan yadda tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufai ke ci gaba da ganawa da manyan shugabannin siyasa daga jam’iyyun SDP, PDP da kuma APC mai mulki.

El-Rufai ya gana da dan takarar gwamnan Jihar Sakkwato a zaben 2023 karkashin tutar jam’iyyar SDP, Sanata Abubakar Gada a gidansa da ke Abuja, inda suka yi buda-baki tare.

  • Tsananin Zafin Rana Na Janyo Mana Cutar Daji – Shugaban Zabaya Na Kaduna
  • Gwamnatin Nasarawa Ta Bukaci Shugaban ALGON Da Ya Daukaka Daarajar Jihar A Idon ‘Yan Nijeriya 

Baya ga Gada da el-Rufai, akwai sauran manyan ‘yan siyasa a wannan ganawa da suka hada da shugaban jam’iyyar SDP, Alhaji Shehu Musa Gabam da tsohon dan majalisar dattawa kuma dan takarar gwamna Jihar Oyo a zaben 2023 na jam’iyyar APC, Sanata Teslim Folarin.

Haka kuma ganawar ta hada har da Sanata Nazif Suleiman, jigo a jam’iyyar PDP daga Jihar Bauchi da Hon. Kamel Akinlabi, tsohon dan majalisar wakilai daga Jihar Oyo shi ma jigo ne a PDP da dai sauran manyan ‘yan siyasa.

Wannan ganawa ta wakana ne kasa da sa’o’I 72 bayan da el-Rufai ya ziyarci sakatariyar jam’iyyar SDP da ke Abuja, inda ya gana da Gabam da sauran jiga-jigan ‘ya’yan jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Bugu da kari, el-Rufa’In ya kuma gana da Sanata Abudul Ningi, wanda Majalisar Dattawa ta dakatar da shi bayan ya yi zargin an yi cushen Naira Triliyan 3 a kasafin 2024.

Idan dai za a iya tunawa, el-Rufai ya bayar da gagarumar gudummawa lokacin yakin neman zaben Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a zaben 2023, sai dai kuma majalisar dattawa ta ki amincewa da shi a matsayin minista sakamakon korafin da ta ce an gabatar mata a kansa.

A irin kwarewa da gogewar siyasarsa, ana ganin yawaitar ganawar da yake yi da ‘yan jam’iyyun adawa na da nasaba da siyasar 2027, kuma ana rade-raden zai iya sauya sheka kamar yadda wata majiya ta bayyana wa LEADERSHIP Hausa.

Majiyar ta ce, “Ko shakka babu haduwar manyan ‘yan siyasan na iya kawo wa Nijeriya sabon fata, musamman a daidai lokacin da mafi yawancin ‘yan kasar nan ke fama da fatara, yunwa, rashin tsaro da dai sauransu.”
Majiyar ta bayyana cewa, Gabam ya siffanta el-Rufai a matsayin abokin da ke da kwarewar siyasa wanda Nijeriya na bukatar shugabanni irin sa.

Majiyar ta kara da cewa Gabam ya yi masa godiya sosai bisa wannan ziyara, inda ya ce a yanzu lokaci ya yi da duk masu ruwa da tsaki a kasar nan za su yi watsi da bambancin kabilanci, yanki da siyasa su rungumi yadda za a ciyar da Nijeriya gaba, musamman a daidai lokacin da kasar ke fuskantar matsaloli da suka hada da yunwa, rashin tsaro, rashin ayyukan yi, garkuwa da mutane, hauhawar farashin kayayyaki da dai sauransu.

Majiyar dai ta boye mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar da suka tarbi el-Rufai.

Har ila yau, wasu rahotanni kuma sun bayyana cewa wannan sabon yunkurin na el-Rufai yana da nasaba da ficewa daga jam’iyyar APC, saboda ana ganin an fusata shi a jam’iyyar bisa rashin ba shi mukamin minista.

Sai dai kuma, el-Rufa’I ya musanta shirin sauya shekar domin tsayawa takarar shugaban kasa a 2027. Mai magana da yawun el-Rufai, Muyiwa Adekeye, ya bayyana cewa ko kadan mai gidansa ba ya shirin kalubalantar Tinubu a zaben 2027.

Mashawarcin tsohon gwamnan ya nesanta mai gidan nasa da komawa wata jam’iyya, yana mai cewa cikin sauki mutane ke zunduma karya kan al’amuran da suka shafi siyasa.

Ya ce a matsayinsa na Dan’adam dole ne ya yi cudanya a tsakanin mutane wadanda ba jam’iyyarsu daya ba, sannan dole a tsakanin mutane a samu ziyarar juna da kuma yin tarayya da juna.

Haka kuma el-rufai ya ce a matsayinsa na jigon APC wanda suka kafa wannan gwamnatin, ba zai manta da abokansa ba wadanda ba sa jam’iyya daya.

Ya kara da cewa ya samu damar yin bude-baki tare da abokansa a wannan ziyara kamar irinsu mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribado, wanda shi dan APC ne da Kashim Imam da kuma shugaban jam’iyyar SDP na kasa.
Ko ma dai mene ne, lokaci ne zai tabbatar yayin da kuma ‘Yan Nijeriya suka zuba ido su ga abin da zai wakana nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Peng Liyuan Ta Gana Da Dalibai Da Malaman Sakandaran Jamus Dake Beijing

Next Post

An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara

An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.