ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hasashe A Kan Sabon Yunkurin el-Rufai Da Zargin Ficewarsa APC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
El-Rufai

A kwanan nan, hankula sun karkata a kan yadda tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufai ke ci gaba da ganawa da manyan shugabannin siyasa daga jam’iyyun SDP, PDP da kuma APC mai mulki.

El-Rufai ya gana da dan takarar gwamnan Jihar Sakkwato a zaben 2023 karkashin tutar jam’iyyar SDP, Sanata Abubakar Gada a gidansa da ke Abuja, inda suka yi buda-baki tare.

  • Tsananin Zafin Rana Na Janyo Mana Cutar Daji – Shugaban Zabaya Na Kaduna
  • Gwamnatin Nasarawa Ta Bukaci Shugaban ALGON Da Ya Daukaka Daarajar Jihar A Idon ‘Yan Nijeriya 

Baya ga Gada da el-Rufai, akwai sauran manyan ‘yan siyasa a wannan ganawa da suka hada da shugaban jam’iyyar SDP, Alhaji Shehu Musa Gabam da tsohon dan majalisar dattawa kuma dan takarar gwamna Jihar Oyo a zaben 2023 na jam’iyyar APC, Sanata Teslim Folarin.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ganawar ta hada har da Sanata Nazif Suleiman, jigo a jam’iyyar PDP daga Jihar Bauchi da Hon. Kamel Akinlabi, tsohon dan majalisar wakilai daga Jihar Oyo shi ma jigo ne a PDP da dai sauran manyan ‘yan siyasa.

Wannan ganawa ta wakana ne kasa da sa’o’I 72 bayan da el-Rufai ya ziyarci sakatariyar jam’iyyar SDP da ke Abuja, inda ya gana da Gabam da sauran jiga-jigan ‘ya’yan jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Bugu da kari, el-Rufa’In ya kuma gana da Sanata Abudul Ningi, wanda Majalisar Dattawa ta dakatar da shi bayan ya yi zargin an yi cushen Naira Triliyan 3 a kasafin 2024.

Idan dai za a iya tunawa, el-Rufai ya bayar da gagarumar gudummawa lokacin yakin neman zaben Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a zaben 2023, sai dai kuma majalisar dattawa ta ki amincewa da shi a matsayin minista sakamakon korafin da ta ce an gabatar mata a kansa.

A irin kwarewa da gogewar siyasarsa, ana ganin yawaitar ganawar da yake yi da ‘yan jam’iyyun adawa na da nasaba da siyasar 2027, kuma ana rade-raden zai iya sauya sheka kamar yadda wata majiya ta bayyana wa LEADERSHIP Hausa.

Majiyar ta ce, “Ko shakka babu haduwar manyan ‘yan siyasan na iya kawo wa Nijeriya sabon fata, musamman a daidai lokacin da mafi yawancin ‘yan kasar nan ke fama da fatara, yunwa, rashin tsaro da dai sauransu.”
Majiyar ta bayyana cewa, Gabam ya siffanta el-Rufai a matsayin abokin da ke da kwarewar siyasa wanda Nijeriya na bukatar shugabanni irin sa.

Majiyar ta kara da cewa Gabam ya yi masa godiya sosai bisa wannan ziyara, inda ya ce a yanzu lokaci ya yi da duk masu ruwa da tsaki a kasar nan za su yi watsi da bambancin kabilanci, yanki da siyasa su rungumi yadda za a ciyar da Nijeriya gaba, musamman a daidai lokacin da kasar ke fuskantar matsaloli da suka hada da yunwa, rashin tsaro, rashin ayyukan yi, garkuwa da mutane, hauhawar farashin kayayyaki da dai sauransu.

Majiyar dai ta boye mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar da suka tarbi el-Rufai.

Har ila yau, wasu rahotanni kuma sun bayyana cewa wannan sabon yunkurin na el-Rufai yana da nasaba da ficewa daga jam’iyyar APC, saboda ana ganin an fusata shi a jam’iyyar bisa rashin ba shi mukamin minista.

Sai dai kuma, el-Rufa’I ya musanta shirin sauya shekar domin tsayawa takarar shugaban kasa a 2027. Mai magana da yawun el-Rufai, Muyiwa Adekeye, ya bayyana cewa ko kadan mai gidansa ba ya shirin kalubalantar Tinubu a zaben 2027.

Mashawarcin tsohon gwamnan ya nesanta mai gidan nasa da komawa wata jam’iyya, yana mai cewa cikin sauki mutane ke zunduma karya kan al’amuran da suka shafi siyasa.

Ya ce a matsayinsa na Dan’adam dole ne ya yi cudanya a tsakanin mutane wadanda ba jam’iyyarsu daya ba, sannan dole a tsakanin mutane a samu ziyarar juna da kuma yin tarayya da juna.

Haka kuma el-rufai ya ce a matsayinsa na jigon APC wanda suka kafa wannan gwamnatin, ba zai manta da abokansa ba wadanda ba sa jam’iyya daya.

Ya kara da cewa ya samu damar yin bude-baki tare da abokansa a wannan ziyara kamar irinsu mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribado, wanda shi dan APC ne da Kashim Imam da kuma shugaban jam’iyyar SDP na kasa.
Ko ma dai mene ne, lokaci ne zai tabbatar yayin da kuma ‘Yan Nijeriya suka zuba ido su ga abin da zai wakana nan gaba.

El-Rufai
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara

An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.