ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hasashe A Kan Sabon Yunkurin el-Rufai Da Zargin Ficewarsa APC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
El-Rufai

A kwanan nan, hankula sun karkata a kan yadda tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufai ke ci gaba da ganawa da manyan shugabannin siyasa daga jam’iyyun SDP, PDP da kuma APC mai mulki.

El-Rufai ya gana da dan takarar gwamnan Jihar Sakkwato a zaben 2023 karkashin tutar jam’iyyar SDP, Sanata Abubakar Gada a gidansa da ke Abuja, inda suka yi buda-baki tare.

  • Tsananin Zafin Rana Na Janyo Mana Cutar Daji – Shugaban Zabaya Na Kaduna
  • Gwamnatin Nasarawa Ta Bukaci Shugaban ALGON Da Ya Daukaka Daarajar Jihar A Idon ‘Yan Nijeriya 

Baya ga Gada da el-Rufai, akwai sauran manyan ‘yan siyasa a wannan ganawa da suka hada da shugaban jam’iyyar SDP, Alhaji Shehu Musa Gabam da tsohon dan majalisar dattawa kuma dan takarar gwamna Jihar Oyo a zaben 2023 na jam’iyyar APC, Sanata Teslim Folarin.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ganawar ta hada har da Sanata Nazif Suleiman, jigo a jam’iyyar PDP daga Jihar Bauchi da Hon. Kamel Akinlabi, tsohon dan majalisar wakilai daga Jihar Oyo shi ma jigo ne a PDP da dai sauran manyan ‘yan siyasa.

Wannan ganawa ta wakana ne kasa da sa’o’I 72 bayan da el-Rufai ya ziyarci sakatariyar jam’iyyar SDP da ke Abuja, inda ya gana da Gabam da sauran jiga-jigan ‘ya’yan jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Bugu da kari, el-Rufa’In ya kuma gana da Sanata Abudul Ningi, wanda Majalisar Dattawa ta dakatar da shi bayan ya yi zargin an yi cushen Naira Triliyan 3 a kasafin 2024.

Idan dai za a iya tunawa, el-Rufai ya bayar da gagarumar gudummawa lokacin yakin neman zaben Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a zaben 2023, sai dai kuma majalisar dattawa ta ki amincewa da shi a matsayin minista sakamakon korafin da ta ce an gabatar mata a kansa.

A irin kwarewa da gogewar siyasarsa, ana ganin yawaitar ganawar da yake yi da ‘yan jam’iyyun adawa na da nasaba da siyasar 2027, kuma ana rade-raden zai iya sauya sheka kamar yadda wata majiya ta bayyana wa LEADERSHIP Hausa.

Majiyar ta ce, “Ko shakka babu haduwar manyan ‘yan siyasan na iya kawo wa Nijeriya sabon fata, musamman a daidai lokacin da mafi yawancin ‘yan kasar nan ke fama da fatara, yunwa, rashin tsaro da dai sauransu.”
Majiyar ta bayyana cewa, Gabam ya siffanta el-Rufai a matsayin abokin da ke da kwarewar siyasa wanda Nijeriya na bukatar shugabanni irin sa.

Majiyar ta kara da cewa Gabam ya yi masa godiya sosai bisa wannan ziyara, inda ya ce a yanzu lokaci ya yi da duk masu ruwa da tsaki a kasar nan za su yi watsi da bambancin kabilanci, yanki da siyasa su rungumi yadda za a ciyar da Nijeriya gaba, musamman a daidai lokacin da kasar ke fuskantar matsaloli da suka hada da yunwa, rashin tsaro, rashin ayyukan yi, garkuwa da mutane, hauhawar farashin kayayyaki da dai sauransu.

Majiyar dai ta boye mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar da suka tarbi el-Rufai.

Har ila yau, wasu rahotanni kuma sun bayyana cewa wannan sabon yunkurin na el-Rufai yana da nasaba da ficewa daga jam’iyyar APC, saboda ana ganin an fusata shi a jam’iyyar bisa rashin ba shi mukamin minista.

Sai dai kuma, el-Rufa’I ya musanta shirin sauya shekar domin tsayawa takarar shugaban kasa a 2027. Mai magana da yawun el-Rufai, Muyiwa Adekeye, ya bayyana cewa ko kadan mai gidansa ba ya shirin kalubalantar Tinubu a zaben 2027.

Mashawarcin tsohon gwamnan ya nesanta mai gidan nasa da komawa wata jam’iyya, yana mai cewa cikin sauki mutane ke zunduma karya kan al’amuran da suka shafi siyasa.

Ya ce a matsayinsa na Dan’adam dole ne ya yi cudanya a tsakanin mutane wadanda ba jam’iyyarsu daya ba, sannan dole a tsakanin mutane a samu ziyarar juna da kuma yin tarayya da juna.

Haka kuma el-rufai ya ce a matsayinsa na jigon APC wanda suka kafa wannan gwamnatin, ba zai manta da abokansa ba wadanda ba sa jam’iyya daya.

Ya kara da cewa ya samu damar yin bude-baki tare da abokansa a wannan ziyara kamar irinsu mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribado, wanda shi dan APC ne da Kashim Imam da kuma shugaban jam’iyyar SDP na kasa.
Ko ma dai mene ne, lokaci ne zai tabbatar yayin da kuma ‘Yan Nijeriya suka zuba ido su ga abin da zai wakana nan gaba.

El-Rufai
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

El-Rufai
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara

An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.