ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
9 months ago
ADC

An sami rudani a yayin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ki amincewa da shugabancin sabuwar jam’iyyar hadaka ta ADC wacce tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark yake jagoranta.

Rahotoni sun nuna cewa shahararrun ‘yan siyasa ne suka amince da ADC a matsayin jam’iyyar adawa da za ta kalubalantar APC da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027.

Hadakar jam’iyyar ta kuma amince da tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark, da tsohon ministan cikin gida, Rauf Aregbesola, a matsayin shugaban riko kwarya da sakatareta na kasa.

ADVERTISEMENT

Wasu daga cikin sanannun mambobin jam’iyyar hadakar a wajen taron da aka yi a Abuja, sun hada da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal da tsofaffin gwamnonin jihojin Kaduna da Ribas, Nasir El-Rufai, Rotimi Amaechi da dai sauransu.

Sai dai kuma INEC ba ta lissafa sunayen sabbin kwamitin zartarwa na kasa na jam’iyyar ba, ciki har da Mark da Aregbesola a shafin adireshinta na internet ba, wanda lamarin ke ci gaban da janyo muhawara.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Mambobin kwamitin zartarwar na ADC da suka hada da Bolaji Abdullahi (Sakataren yada labarai na kasa), Babachir Lawal (Mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin arewa maso gabas), Usani Uguru Usani (Mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa), Farfesa Oserheimen Osunbor (Babban lauyan jam’iyyar na kasa), Bar Chinedu Idigbo (Sakataren shirye-shiryen jam’iyyar na kasa), Sen. Musa Elayo (Mataimakin shugaban jam’iyyar na kasar waje) da Kwamared Nkem Ukandu (Sakataren jin dadi da walwala na jam’iyyar na kasa) da sauransu.

Duk da haka, INEC ba ta ki amincewa da sabbin shugabannin tare da kin saka sunayensu da hotunansu a shafinta na yanar gizo. Wannan lamari na ci gaban da damun mambobin jam’iyyar da magoya baya, yana nuna matsaloli a cikin jam’iyyar kafin 2027.

Sai dai yayin da yake mayar da martani ga wannan lamarin, sakataren yada labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya shaida cewa INEC na bin ka’idojin aikinta ne, yana mai jaddada cewa za a warware rudanin a wannan makon.

Abdullahi, wanda ya kasance tsohon minista ya ce, “Abin da ke faruwa kawai shi ne bin ka’idoin aiki, hakika babu wani abu a ciki. Muna bukatar mu aika da wasu sa hannun kuma komi zai yi daidai.

“Jinkirin yana da alaka da ka’idojin gudanarwa ne kawai. Babu batun siyasah ko wani abu. Kawai yana da alaka ne da ka’idodin gudanarwa kuma za a shawo kan wannan lamari. Jinkirin yana da alaka da hanyoyin aiki kawai kuma zan iya gaya maka cewa a shawo kan lamarin a cikin wannan makon.”

Tun lokacin da aka kirkiri hadakar, shugabancin jam’iyyar yana ta samun suka tare da fadawa cikin rikice-rikice da ke tasowa a cikin jam’iyyar.

Masana sun cewa da tun lokacin da aka kafa kwamitin zatarwa karkashin jagorancin Mark, tsohon dan takarar shugaban kasa na ADC, Dumebi Kachikwu, ya kalubalanci kwamitin tare da bayyana Dabid Mark a matsayin shugaba na kawo rarrabuwar kai a jam’iyyar.

Yayin da yake tattaunawa da ‘yan jarida, Kachikwu ya zargi cewa an tilasta wa Mark zama shugaban wani bangare na ADC.

Kachikwu ya ce rashin adalci ne ga ‘yan Nijeriya a ce Atiku da Aregbesola da Mark su jagoranci hadakar jam’iyyar.

“Wannan wata barazana ce ga ‘yan Nijeriya da kuma mambobin jam’iyyar su kira Dabid Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC. Ba shi ba ne shugaba. Ba zai iya zama ba. Mutanen da suka shigo jam’iyyar ta barauniyar hanya bai kamata su shugabanci jam’iyyarmu ba. Ba za mu kasa a gwiwa ba, duk da irin yakarmu da ake yi,” in ji shi.

Hazlika, tsohon dan takarar gwamna na ADC a Jihar Gombe, Nafiu Bala, ya bayyana cewa fatawar jam’iyyar a hannun Mark da Aregbesola ya saba wa dimokuradiyya kuma ya yi alkawarin yin gwagwarmaya a kan yakar lamarin.

Ya zargi Nwosu da sauran tsofaffin shugabannin jam’iyyar kan watsi da nauyin da aka dora musu kan tafiyar da harkokin jam’iiyyar kamar yadda tsarin mulki ya tanada.

Haka kuma Bala ya bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na wucin gadi tun da Nwosu ya yi murabus.

A yayin da yake mayar da martani ga wannan lamari, Nwosu ya shaida wace cewa rikicin shugabanci a jam’iyyar shiryayyan abu ne, yana zargin cewa akwai wadanda suke yin aiki ga fadar shugaban kasa, wanda yanzu suna cikin tashin hankali game da ADC.

“Zan ba da shawara ga ‘yan siyasa su mai da hankali kan bayar da ribar dimokuradiyya ga mutanensu, sannan su shirya don zabe mai zuwz maimakon lalata tsarin zabe ta haramtacciyar hanya,” in ji shi.

ADC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
ADC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.