ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
10 months ago
PDP

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya gargadi cewa jam’iyyar PDP za ta fuskantanci hadarin tarwatsewa idan ta yi kokarin dawo da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi a cikin jikinta kafin zaben 2027.

 

A yayin wata tattaunawarsa tare da ‘yan jarida, Wike ya ce PDP ba ta dauki darasi ba game da kuskurenta na baya wadanda suka janyo mata rashin nasara a zaben 2023.

ADVERTISEMENT
  • An Shiga Damuwa Yayin Da Gwamnatin Nijeriya Ke Jinkiri Wajen Biyan ‘Yan Kwangila
  • Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

Ya tunatar da cewa shi da sauran shugabannin jam’iyyar sun sake maimaita wanjen kuskuren na bari dan takarar shugaban kasa da shugaban jam’iyyar na kasa su fito daga yankin arewacin Nijeriya, wannan wani mataki ne na wanda ya saba da tsarin siyasar kasar nan.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Tun daga ranar farko, na gaya wa abokan aikina da ke cikin jam’iyyar PDP cewa kuna daba wa cikinku wuka. Idan kuka bari abubuwan da ke faruwa su ci gaba a haka, za ji a jikinku. Kuma me na ce? Ba za ku iya fitar da dan takarar shugaban kasa da shugaban jam’iyya na kasa su fito a yankin guda ba,” in ji Wike.

 

Tsohon gwamnan Jihar Ribas ya zargi PDP da rashin yin adalci wajen rarraba mukamai da kuma watsi da kiraye-kirayen yin adalci da daidaito, a cewarsa, wannan mataki su ne makasudin rashin nasarar jam’iyyar a zaben bara.

 

“Yana da kyau tun yanzu a warwaren matsalar tikitin takarar shugaban kasa kuma na shugaban jam’iyyar na kasa n. A gani na hakan shi ya fi dacewa. Kuma shi ne adalci a siyasance. Ba na yin dana sani a kan haka,” ya bayyana.

 

Wike ya jaddada cewa dole ne shugabancin kasar nan ya sake komawa yankin kudu don tabbatar da adalci da daidaito a cikin harkokin siyasar Nijeriya.

 

A cewarsa, girman kai da kin sauraron gaskiya daga wasu shugabannin PDP sun sa jam’iyyar taraunata, sannan kuma ta samu rashin karfi tare rasa samun mulki.

 

Ya kuma musanta maganganun da suka shafi yiwuwar dawowar Obi cikin PDP, yana bayyana wannan mataki a matsayin mai tsananin hadari a cikin jam’iyyar.

 

“Ta wani dalili za ku dawo mana da Obi cikin wannan jam’iyyar? Kana son kashe jam’iyyar ne? Obi wanda yake zagin jam’iyyar, yana cewa ta lalace, yanzu kuma jam’iyyar ta zama mai kyau a gare shi ne? Burin mutum na iya sa mutane su kasance har zuwa gidan Shaidan,” in ji Wike.

Ministan ya kara jaddada cewa irin wannan hukunci zai kara lalata ingancin jam’iyyar kuma zai tarwatsa duk wata ginshikin da ya rage a cikin jam’iyyar a halin yanzu.

Ya ce, “Idan kana son tarwatsa jam’iyyar ne, to zai ka gaggauta shigo da Obi cikin jam’iyyar. Babu wata hanya da zai dawo saboda burinsa na kashin kai. Babu dabara da kuma ka’ida a wannan mataki,” ya kara bayyanawa.

Wike ya ci gaba da cewa yana tsaye kan matsayinsa cewa a yi adalci da gaskiya da kuma bin tsarin karba-karba domin ta wannan hanya ce kadai jam’iyyar PDP za ta sau damar dawo da tasirinta a kasar nan.

PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • Sulaiman
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam
PDP
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.