• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Masu Amfani Da Yanar Gizo Ta Intanet A Amurka Suka Yi Wa Janet Yellen Dariya Kan Kalamanta Masu Ban Mamaki?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Masu Amfani Da Yanar Gizo Ta Intanet A Amurka Suka Yi Wa Janet Yellen Dariya Kan Kalamanta Masu Ban Mamaki?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da take ziyara a wata masana’antar kera batir bisa karfin hasken rana dake jihar Georgia a kasar Amurka kwanan nan, sakatariyar kudin kasar, Janet L. Yellen, ta bayyana cewa, sana’ar bunkasa sabbin makamashi ta kasar Sin na fuskantar matsala, wato yawan hajojin da ake samarwa ya wuce yawan bukatun da ake da su, al’amarin da ya jirkita farashin kayayyaki gami da salon samar da su a duk duniya, tare kuma da kawo illa ga muradun kamfanoni gami da ma’aikatan kasar ta Amurka. Game da wannan batu, Yellen ta ce za ta dauki matakan kare kamfanoni gami da ma’aikatan Amurka, don su shiga takara cikin wani dandali “mai adalci”.

Irin wadannan kalamai na Janet Yellen sun janyo dariya daga masu amfani da yanar gizo ta Intanet a Amurka, inda suka ce, tun farko Yellen ta ce kasar Sin ta gaza a fannin raya makamashi mai tsafta, amma yanzu ta fara zargin kasar da cewa ta wuce gona da iri. To, me ya sa Amurka ba za ta iya yin shiru, ta yi harkar gabanta ba? Wasu kuma sun ce, da Amurka tana da fifiko a fagen takara, to za ta ce a raya kasuwa marar shinge, amma tun da ba ta da shi, za ta koma ga ra’ayin bada kariya ga harkokin cinikayya. Ke nan wannan ita ce ka’idar Amurka.

  • Sin Da EU Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Domin Inganta Musaya Tsakanin Jama’arsu
  • Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

A shekara ta 2023, jimillar darajar wasu sabbin hajoji uku kirar kasar Sin da aka fitar zuwa kasashen ketare ta zarce kudin kasar wato Yuan tiriliyan 1.06, ciki har da motoci masu amfani da makamashin wutar lantarki, da batir irin na lithium-ions, gami da batir mai amfani da makamashin hasken rana. Ba karfin tattalin arzikin da kasar Sin ke da shi kawai wannan abun ya nuna ba, har da taimakawa sauran kasashe komawa kan raya makamashi mai tsafta, al’amarin da ya bayar da babbar gudummawa ga tinkarar sauyin yanayin dake addabar duniya.

Amma a ra’ayin wasu ‘yan siyasar Amurka, sabbin sana’o’in kasar Sin na bunkasa cikin sauri, abun dake illata moriyarsu. To, yaya za su yi? Abun da suka yi ba kyautata fasahohi don inganta karfinsu na yin takara ba ne, suna yunkurin shafawa kasar Sin bakin fenti, da kawo cikas, da keta hakkin al’ummar kasar na samar da ci gaba, bisa hujjojin “tsaron kasa”, ko kuma “yawan hajojin da ake samarwa ya wuce yawan bukatun da ake da su”.

Wasu kwararru na kungiyar masana ta Brookings Institution dake Amurka na ganin cewa, hadin-gwiwar Sin da Amurka da ta shafi fasahohin makamashi mai tsafta, ka iya taimaka musu wajen rage fitar da iska mai gurbata muhalli, da kara samun fahimtar juna a tsakaninsu. Kaza lika, sun ce, idan kuma aka maida wannan bangaren a matsayin wani filin yin takara na daban, za’a kawo babbar illa ga aikin samar da kayayyaki a duk duniya gami da ajandar tinkarar sauyin yanayi. (Murtala Zhang)

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da EU Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Domin Inganta Musaya Tsakanin Jama’arsu

Next Post

Dambarwar Amal Umar Da ‘Yansanda, Ina Aka Kwana?

Related

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

57 minutes ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

1 hour ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

3 hours ago
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

4 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

22 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

23 hours ago
Next Post
Amal Umar Ta Gurfana A Gaban Kotu Akan Zargin Bai Wa ‘Yansanda Cin Hanci

Dambarwar Amal Umar Da 'Yansanda, Ina Aka Kwana?

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.