ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Masu Amfani Da Yanar Gizo Ta Intanet A Amurka Suka Yi Wa Janet Yellen Dariya Kan Kalamanta Masu Ban Mamaki?

by CGTN Hausa
2 years ago
Yanar gizo

Yayin da take ziyara a wata masana’antar kera batir bisa karfin hasken rana dake jihar Georgia a kasar Amurka kwanan nan, sakatariyar kudin kasar, Janet L. Yellen, ta bayyana cewa, sana’ar bunkasa sabbin makamashi ta kasar Sin na fuskantar matsala, wato yawan hajojin da ake samarwa ya wuce yawan bukatun da ake da su, al’amarin da ya jirkita farashin kayayyaki gami da salon samar da su a duk duniya, tare kuma da kawo illa ga muradun kamfanoni gami da ma’aikatan kasar ta Amurka. Game da wannan batu, Yellen ta ce za ta dauki matakan kare kamfanoni gami da ma’aikatan Amurka, don su shiga takara cikin wani dandali “mai adalci”.

Irin wadannan kalamai na Janet Yellen sun janyo dariya daga masu amfani da yanar gizo ta Intanet a Amurka, inda suka ce, tun farko Yellen ta ce kasar Sin ta gaza a fannin raya makamashi mai tsafta, amma yanzu ta fara zargin kasar da cewa ta wuce gona da iri. To, me ya sa Amurka ba za ta iya yin shiru, ta yi harkar gabanta ba? Wasu kuma sun ce, da Amurka tana da fifiko a fagen takara, to za ta ce a raya kasuwa marar shinge, amma tun da ba ta da shi, za ta koma ga ra’ayin bada kariya ga harkokin cinikayya. Ke nan wannan ita ce ka’idar Amurka.

  • Sin Da EU Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Domin Inganta Musaya Tsakanin Jama’arsu
  • Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

A shekara ta 2023, jimillar darajar wasu sabbin hajoji uku kirar kasar Sin da aka fitar zuwa kasashen ketare ta zarce kudin kasar wato Yuan tiriliyan 1.06, ciki har da motoci masu amfani da makamashin wutar lantarki, da batir irin na lithium-ions, gami da batir mai amfani da makamashin hasken rana. Ba karfin tattalin arzikin da kasar Sin ke da shi kawai wannan abun ya nuna ba, har da taimakawa sauran kasashe komawa kan raya makamashi mai tsafta, al’amarin da ya bayar da babbar gudummawa ga tinkarar sauyin yanayin dake addabar duniya.

ADVERTISEMENT

Amma a ra’ayin wasu ‘yan siyasar Amurka, sabbin sana’o’in kasar Sin na bunkasa cikin sauri, abun dake illata moriyarsu. To, yaya za su yi? Abun da suka yi ba kyautata fasahohi don inganta karfinsu na yin takara ba ne, suna yunkurin shafawa kasar Sin bakin fenti, da kawo cikas, da keta hakkin al’ummar kasar na samar da ci gaba, bisa hujjojin “tsaron kasa”, ko kuma “yawan hajojin da ake samarwa ya wuce yawan bukatun da ake da su”.

Wasu kwararru na kungiyar masana ta Brookings Institution dake Amurka na ganin cewa, hadin-gwiwar Sin da Amurka da ta shafi fasahohin makamashi mai tsafta, ka iya taimaka musu wajen rage fitar da iska mai gurbata muhalli, da kara samun fahimtar juna a tsakaninsu. Kaza lika, sun ce, idan kuma aka maida wannan bangaren a matsayin wani filin yin takara na daban, za’a kawo babbar illa ga aikin samar da kayayyaki a duk duniya gami da ajandar tinkarar sauyin yanayi. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Yanar gizo
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
Amal Umar Ta Gurfana A Gaban Kotu Akan Zargin Bai Wa ‘Yansanda Cin Hanci

Dambarwar Amal Umar Da 'Yansanda, Ina Aka Kwana?

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.