ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Masu Amfani Da Yanar Gizo Ta Intanet A Amurka Suka Yi Wa Janet Yellen Dariya Kan Kalamanta Masu Ban Mamaki?

by CGTN Hausa
2 years ago
Yanar gizo

Yayin da take ziyara a wata masana’antar kera batir bisa karfin hasken rana dake jihar Georgia a kasar Amurka kwanan nan, sakatariyar kudin kasar, Janet L. Yellen, ta bayyana cewa, sana’ar bunkasa sabbin makamashi ta kasar Sin na fuskantar matsala, wato yawan hajojin da ake samarwa ya wuce yawan bukatun da ake da su, al’amarin da ya jirkita farashin kayayyaki gami da salon samar da su a duk duniya, tare kuma da kawo illa ga muradun kamfanoni gami da ma’aikatan kasar ta Amurka. Game da wannan batu, Yellen ta ce za ta dauki matakan kare kamfanoni gami da ma’aikatan Amurka, don su shiga takara cikin wani dandali “mai adalci”.

Irin wadannan kalamai na Janet Yellen sun janyo dariya daga masu amfani da yanar gizo ta Intanet a Amurka, inda suka ce, tun farko Yellen ta ce kasar Sin ta gaza a fannin raya makamashi mai tsafta, amma yanzu ta fara zargin kasar da cewa ta wuce gona da iri. To, me ya sa Amurka ba za ta iya yin shiru, ta yi harkar gabanta ba? Wasu kuma sun ce, da Amurka tana da fifiko a fagen takara, to za ta ce a raya kasuwa marar shinge, amma tun da ba ta da shi, za ta koma ga ra’ayin bada kariya ga harkokin cinikayya. Ke nan wannan ita ce ka’idar Amurka.

  • Sin Da EU Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Domin Inganta Musaya Tsakanin Jama’arsu
  • Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

A shekara ta 2023, jimillar darajar wasu sabbin hajoji uku kirar kasar Sin da aka fitar zuwa kasashen ketare ta zarce kudin kasar wato Yuan tiriliyan 1.06, ciki har da motoci masu amfani da makamashin wutar lantarki, da batir irin na lithium-ions, gami da batir mai amfani da makamashin hasken rana. Ba karfin tattalin arzikin da kasar Sin ke da shi kawai wannan abun ya nuna ba, har da taimakawa sauran kasashe komawa kan raya makamashi mai tsafta, al’amarin da ya bayar da babbar gudummawa ga tinkarar sauyin yanayin dake addabar duniya.

ADVERTISEMENT

Amma a ra’ayin wasu ‘yan siyasar Amurka, sabbin sana’o’in kasar Sin na bunkasa cikin sauri, abun dake illata moriyarsu. To, yaya za su yi? Abun da suka yi ba kyautata fasahohi don inganta karfinsu na yin takara ba ne, suna yunkurin shafawa kasar Sin bakin fenti, da kawo cikas, da keta hakkin al’ummar kasar na samar da ci gaba, bisa hujjojin “tsaron kasa”, ko kuma “yawan hajojin da ake samarwa ya wuce yawan bukatun da ake da su”.

Wasu kwararru na kungiyar masana ta Brookings Institution dake Amurka na ganin cewa, hadin-gwiwar Sin da Amurka da ta shafi fasahohin makamashi mai tsafta, ka iya taimaka musu wajen rage fitar da iska mai gurbata muhalli, da kara samun fahimtar juna a tsakaninsu. Kaza lika, sun ce, idan kuma aka maida wannan bangaren a matsayin wani filin yin takara na daban, za’a kawo babbar illa ga aikin samar da kayayyaki a duk duniya gami da ajandar tinkarar sauyin yanayi. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Yanar gizo
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Amal Umar Ta Gurfana A Gaban Kotu Akan Zargin Bai Wa ‘Yansanda Cin Hanci

Dambarwar Amal Umar Da 'Yansanda, Ina Aka Kwana?

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.