• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar da ta gabata, tun da sanyin safe matasa da mata da tsoffafi har da matan aure suka far ma sauran buhunan shinkafar Dangote da aka kai tallafi Jihar Kebbi inda suka wawashe akalla buhu dubu biyu.

Bayan samun wannan labarin abin da matasa da sauran jama’a suka aikata jami’an tsaro sun kawo dauki na gaggawa don ganin jama’a ba su wawashe shinkafar ba. Jami’an tsaro sun yi iya kokarisu wajen mai do da shinkafar da aka wawashe.

  • Karin kudin Aikin Hajji: Gwamnatin Kebbi Za Ta Tallafawa Kowanne Maniyyaci Da Naira Miliyan 1
  • Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da Murabus Din Babban Limamin Masallacin Wala

Bayan aukuwar wannan ne, duk dai a ranar da misalin karfe daya na dare jama’a suka sake fitowa suka fasa rumbun ajiyar abincin da karamar hukumar Birnin Kebbi ta ajiye da zimmar rabawa ga jama’arta washe garin ranar Lahadi. A nan ma jami’an tsaron ‘yansanda da na Sojoji sun yi iya kokarinsu na ganin cewa jama’a basu wawashe dukkan abincin ba ta hanyar sanya barkonon tsohuwa amma duk da hakan bai hana aka wawashe wani sashe daga cikin abincin ba.

Yanzu hakan, a Jihar ta kebbi akwai labarin cewa jami’an tsaro sun samu nasarar cafke wasu daga cikin jama’ar da ake zargi da wawashe rumbun da kuma na wata mota a kusa dakasuwar kara da ke cikin garin Birnin Kebbi.

Ganin yadda abin ya auku bi da bi, sai ‘yansanda suka fantsama farautar mutanen da ake zargi da wawashe abincin. Bisa ga hakan hankalin jama’a a garin na Birnin Kebbi ya tashi, inda jama’a da dama suka shiga tsoro da farga.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Bugu da kari, bayan wuni daya an samu zaman lafiya a sassan Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi, sai kuma a washegari, dubban mutane ne suka tattara kansu tare da kutsawa cikin shagunan ‘yan kasuwa masu sayar da shinkafa da sauran hatsi iri-iri a unguwar Bayan-Kara, suka kwashe daruruwan buhuna.

Wani matashi, Abu Wanzan ya bayyana wa wakilinmu cewa, “yunwa da fatara ne suka sa jama’a suka kai hari kan wajen da ake ajiye abinci, haka kuma ba mu ji dadin yadda aka fara raba kayan abinci na baya-bayan nan da gwamnati ta sayo wa al’ummar jihar ba. Da yawa mazauna yankin garin Birnin Kebbi har yanzu ba su amfana da abincin da Gwamna Nasir Idris ya ce za a raba ma jama’a ba.”

Bisa abin da ya faru, ofishin mataimakin gwamnan jihar ya fitar da sanarwa, ta nuna rashin jin dadi game da lamarin tare da bayar da tabbacin cewa an dauki tsauraran matakan tsaro domin dakile sake afkuwar lamarin.

Hakazalika kwamishinan yada labarai da al’adu Alhaji Yakubu Ahmad Birnin Kebbi, ya sanar wa manema labaru da kafa kwamitin mutane 13 a karkashin jagorancin kwamishinan ma’aikatar gona domin gudanar da bincike kan lamarin, wanda gwamnati ta bayyana a matsayin abin takaici da zargi.

Shi ma da yake jawabi ga manema labarai kwamishinan Ma’aikatar aikin goma da albarkatun kasa Alhaji Shehu Mu’azu ya bayyana cewa yawancin shinkafar da aka kwashe daga dakin ajiyar kaya dake Bayan-Kara mallakin karamar hukumar Birnin Kebbi ne a wani bangare na tallafin da gwamnatin jihar ta raba wa Kananan hukumomin 21na jhar.

Ya ce jami’an tsaro sun yi nasarar kwato buhunan abincin sama da 2,000 daga hannun jama’a tare da mayar da su inda aka ajiye su.

Alhaji Shehu Mu’azu wanda shi ne shugaban kwamitin binciken ya shaida wa manema labarai cewa an ba ‘yan kwamitinsa wa’adin kwanaki biyar daga ranar Litinin zuwa Juma’a domin su binciki musabbabin faruwar lamarin, da gano mutane ko kungiyoyin da ke da hannu tare da ba gwamnati shawara yadda ya kamata don kiyaye afkuwar lamarin.

A ranar Alhamis 21 ga watann Maris, ne Gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, ya kaddamar da rabon tallafin abinci da suka hada da shinkafa, Dawa da sauran hatsi domin tausaya wa jama’ar jihar a watan Azumin Ramadan.

Bayan makonni kadan da ya kaddamar da rabon tallafin abincin ne kuma sai Gidauniyar Dangote ta bayyana nata rabon tallafin wanda daga bisani aka daka wawa a ragowar da ba a kai ga rabarwa ba ga al’ummar jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jerin Manyan Attajiran Nijeriya A 2024

Next Post

Gwamna Uba Ya Umarci Kamo ‘Yan Kwangilar Da Suka Fara Aiki Suka Gudu

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
Kaduna

Gwamna Uba Ya Umarci Kamo 'Yan Kwangilar Da Suka Fara Aiki Suka Gudu

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.