• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sakon Sallah: Gwamna Nasir Ya Yi Kira Da Hadin Kai Don Gina Jihar Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Sakon Sallah: Gwamna Nasir Ya Yi Kira Da Hadin Kai Don Gina Jihar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, ya bukaci jam’iyyun adawa da su hada kai da gwamnatinsa domin gina kyakkyawan shugabanci da bunkasa tattalin arzikin jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a fadar gwamnati da ke Birnin Kebbi a sakonsa na fatan alheri ga al’ummar jihar bayan halartar Sallar Eid-el-Fitr a babban masallacin Sallar Idi a Birnin Kebbi.

  • Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000
  • Basarake Ya Rasu Bayan Idar Da Sallar Idi A Legas

“Yanzu da aka kammala zabe da siyasa, ina gayyatar al’ummar jihar na kowane bangare ba tare da la’akari na jam’iyya ba. Mu hada kai na gani ci gaban jihar mu domin kaiwa ga matakin ci gaban da ake so”.

“Mafi yawan jama’a sun zabe ni, ina gode musu da sauran su bisa goyon bayan da suka ba ni, da aminci da kuma hadin kai,” inji shi.

Ya tabbatar da cewa gwamnati za ta tabbatar da samar da ababen more rayuwa, tattalin arziki, noma, bunkasa ilimi da samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

“Babban asibitocin da ke Argungu, Yauri da Zuru, za a gyara su tare da samar da kayan aiki na zamani don yi wa mazauna yankin hidima da kuma gudanar da ayyukansu a matsayin cibiyoyin kiwon lafiya ba tare da sun kawo masara lafiya a babban birnin Jihar ba” in ji shi.

Ya taya al’ummar jihar Kebbi murnar kammala azumin watan Ramadan da kuma murnar bukukuwan karamar Sallah.

Gwamna Nasir

Dakta Nasir Idris ya bukace su da su ci gaba da gudanar da addu’o’i na musamman domin samun nasarar gwamnati, zaman lafiya, tsaro da ci gaban al’umma.

Gwamnan ya kara da bayyana gamsuwarsa game da dawowar tsaro a yankin Kebbi ta Kudu wanda hakan ya sa manoman za su koma gonakinsu domin gudanar aikin noman rani da damana.

A nasa jawabin, karamin ministan ilimi, Dakta Tanko Yusuf Sununu, wanda ya yi Sallar Idi tare da Gwamna Nasir Idris, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su ci gaba da yi wa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu addu’a domin samun nasara a matakin tarayya da jihohin kasar nan.

Dokta Sununu ya bayyana Gwamna Nasir Idris a matsayin shugaba mai iya gudanar da mulki kamar yadda irin ci gaban da aka samu tun hawan mulkinsa zuwa yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Ma Ying-Jeou A Beijing

Next Post

Yawan Motocin Da Sin Ta Sayar Ya Kai Miliyan 6.72 A Rubu’in Farkon Bana

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

10 minutes ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

2 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

2 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

3 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

6 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

8 hours ago
Next Post
Yawan Motocin Da Sin Ta Sayar Ya Kai Miliyan 6.72 A Rubu’in Farkon Bana

Yawan Motocin Da Sin Ta Sayar Ya Kai Miliyan 6.72 A Rubu’in Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.