• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Ziyarar Antony Blinken A Kasar Sin Za Ta Banbanta Da Ta Sauran Jami’an Amurka?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ko Ziyarar Antony Blinken A Kasar Sin Za Ta Banbanta Da Ta Sauran Jami’an Amurka?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yawa daga masu fashin baki na hasashen cewa, mawuyaci ne a samu wani babban sauyi a ziyarar da sakataren wajen Amurka Antony Blinken zai gudanar a kasar Sin, tsakanin ranar Laraba zuwa Jumma’a, musamman duba da cewa an shiga shekarar babban zaben shugabancin Amurka, irin lokacin da abun da kadai ke hade kan manyan jam’iyyun kasar wato Democrat da Republican, shi ne sukar kasar Sin domin jan ra’ayin Amurkawa da samun kuri’u, amma duk da haka, yana da kyau, ganin babban jami’in na Amurka zai gudanar da ziyara a kasar Sin a irin wannan lokaci. 

Haka dai abun yake, idan mun waiwayi ziyarar da sakatariyar cinikayyar Amurka Gina Raimondo ta gudanar a kasar Sin a shekarar bara, da wadda sakatariyar baitul-malin Amurka Janet Yellen ta gudanar a farkon watan nan na Afirilu, da ma dawo da tattaunawa ta kafar bidiyo tsakanin ministocin tsaro na kasashen biyu, wato Lloyd Austin, da takwaran aikinsa na Sin Dong Jun a farkon watan nan.

  • Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?
  • Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci

Ko shakka babu, Bahaushe kan ce “Yawan gaisuwa ya fi yawan fada”, wato dai yawan tattaunawa tsakanin sassan biyu, ya fi a ce ana zaman doya da man ja, to amma kuma yawaitar matakan takunkumi kan kamfanonin Sin, da shafawa Sin din kashin kaji da Amurka ke yi, yana bayyana akasin kalaman neman hadin kai da jami’an Amurkan ke furtawa.

Akwai tarin ayyuka da ya dace a gudanar, domin kyautata dangantakar Sin da Amurka, da kuma matakai na kaucewa ci gaba da tabarbarewar alakar tattalin arziki da siyasa tsakanin sassan biyu.

Da farko dai, wajibi ne a yi watsi da batun “Raba Gari”. Kuma hakan zai tabbata ne kawai idan har Amurka ta yi fatali da kokarin danne kamfanonin Sin, irin su babban kamfanin fasahohin sadarwa na Huawei, da fakewa da batun “Tsaron Kasa”, don baiwa kasuwar Amurka kariyar cinikayya, da shawo kan batun haramtawa kamfanonin kirar sassan laturoni na “Chips” na Amurka sayar da hajojin su ga kasuwannin Sin da dai saura su.

Labarai Masu Nasaba

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Maimakon daukar matakan zargi, da danniya, da kariyar cinikayya da nuna son kai, kamata ya yi Amurka ta hada gwiwa da kasar Sin, da ma sauran kasashen duniya, wajen gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, ta yadda moriyar bai daya ta dukkanin sassa za ta zarce ta kashin kai. A daya bangaren kuma, nuna fuska biyu, da fada ba cikawa, ba abun da za su haifar illa raba kawuna, da gurgunta amincewa da juna, da lalata moriyar duniya baki daya.( Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

Next Post

Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

Related

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
Daga Birnin Sin

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

8 minutes ago
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

20 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

21 hours ago
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

22 hours ago
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

2 days ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

2 days ago
Next Post
Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

LABARAI MASU NASABA

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

August 11, 2025
Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.