ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Ziyarar Antony Blinken A Kasar Sin Za Ta Banbanta Da Ta Sauran Jami’an Amurka?

by CGTN Hausa
2 years ago
Blinken

Da yawa daga masu fashin baki na hasashen cewa, mawuyaci ne a samu wani babban sauyi a ziyarar da sakataren wajen Amurka Antony Blinken zai gudanar a kasar Sin, tsakanin ranar Laraba zuwa Jumma’a, musamman duba da cewa an shiga shekarar babban zaben shugabancin Amurka, irin lokacin da abun da kadai ke hade kan manyan jam’iyyun kasar wato Democrat da Republican, shi ne sukar kasar Sin domin jan ra’ayin Amurkawa da samun kuri’u, amma duk da haka, yana da kyau, ganin babban jami’in na Amurka zai gudanar da ziyara a kasar Sin a irin wannan lokaci. 

Haka dai abun yake, idan mun waiwayi ziyarar da sakatariyar cinikayyar Amurka Gina Raimondo ta gudanar a kasar Sin a shekarar bara, da wadda sakatariyar baitul-malin Amurka Janet Yellen ta gudanar a farkon watan nan na Afirilu, da ma dawo da tattaunawa ta kafar bidiyo tsakanin ministocin tsaro na kasashen biyu, wato Lloyd Austin, da takwaran aikinsa na Sin Dong Jun a farkon watan nan.

  • Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?
  • Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci

Ko shakka babu, Bahaushe kan ce “Yawan gaisuwa ya fi yawan fada”, wato dai yawan tattaunawa tsakanin sassan biyu, ya fi a ce ana zaman doya da man ja, to amma kuma yawaitar matakan takunkumi kan kamfanonin Sin, da shafawa Sin din kashin kaji da Amurka ke yi, yana bayyana akasin kalaman neman hadin kai da jami’an Amurkan ke furtawa.

ADVERTISEMENT

Akwai tarin ayyuka da ya dace a gudanar, domin kyautata dangantakar Sin da Amurka, da kuma matakai na kaucewa ci gaba da tabarbarewar alakar tattalin arziki da siyasa tsakanin sassan biyu.

Da farko dai, wajibi ne a yi watsi da batun “Raba Gari”. Kuma hakan zai tabbata ne kawai idan har Amurka ta yi fatali da kokarin danne kamfanonin Sin, irin su babban kamfanin fasahohin sadarwa na Huawei, da fakewa da batun “Tsaron Kasa”, don baiwa kasuwar Amurka kariyar cinikayya, da shawo kan batun haramtawa kamfanonin kirar sassan laturoni na “Chips” na Amurka sayar da hajojin su ga kasuwannin Sin da dai saura su.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Maimakon daukar matakan zargi, da danniya, da kariyar cinikayya da nuna son kai, kamata ya yi Amurka ta hada gwiwa da kasar Sin, da ma sauran kasashen duniya, wajen gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, ta yadda moriyar bai daya ta dukkanin sassa za ta zarce ta kashin kai. A daya bangaren kuma, nuna fuska biyu, da fada ba cikawa, ba abun da za su haifar illa raba kawuna, da gurgunta amincewa da juna, da lalata moriyar duniya baki daya.( Saminu Alhassan)

Blinken
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.