ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Ziyarar Antony Blinken A Kasar Sin Za Ta Banbanta Da Ta Sauran Jami’an Amurka?

by CGTN Hausa
2 years ago
Blinken

Da yawa daga masu fashin baki na hasashen cewa, mawuyaci ne a samu wani babban sauyi a ziyarar da sakataren wajen Amurka Antony Blinken zai gudanar a kasar Sin, tsakanin ranar Laraba zuwa Jumma’a, musamman duba da cewa an shiga shekarar babban zaben shugabancin Amurka, irin lokacin da abun da kadai ke hade kan manyan jam’iyyun kasar wato Democrat da Republican, shi ne sukar kasar Sin domin jan ra’ayin Amurkawa da samun kuri’u, amma duk da haka, yana da kyau, ganin babban jami’in na Amurka zai gudanar da ziyara a kasar Sin a irin wannan lokaci. 

Haka dai abun yake, idan mun waiwayi ziyarar da sakatariyar cinikayyar Amurka Gina Raimondo ta gudanar a kasar Sin a shekarar bara, da wadda sakatariyar baitul-malin Amurka Janet Yellen ta gudanar a farkon watan nan na Afirilu, da ma dawo da tattaunawa ta kafar bidiyo tsakanin ministocin tsaro na kasashen biyu, wato Lloyd Austin, da takwaran aikinsa na Sin Dong Jun a farkon watan nan.

  • Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?
  • Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci

Ko shakka babu, Bahaushe kan ce “Yawan gaisuwa ya fi yawan fada”, wato dai yawan tattaunawa tsakanin sassan biyu, ya fi a ce ana zaman doya da man ja, to amma kuma yawaitar matakan takunkumi kan kamfanonin Sin, da shafawa Sin din kashin kaji da Amurka ke yi, yana bayyana akasin kalaman neman hadin kai da jami’an Amurkan ke furtawa.

ADVERTISEMENT

Akwai tarin ayyuka da ya dace a gudanar, domin kyautata dangantakar Sin da Amurka, da kuma matakai na kaucewa ci gaba da tabarbarewar alakar tattalin arziki da siyasa tsakanin sassan biyu.

Da farko dai, wajibi ne a yi watsi da batun “Raba Gari”. Kuma hakan zai tabbata ne kawai idan har Amurka ta yi fatali da kokarin danne kamfanonin Sin, irin su babban kamfanin fasahohin sadarwa na Huawei, da fakewa da batun “Tsaron Kasa”, don baiwa kasuwar Amurka kariyar cinikayya, da shawo kan batun haramtawa kamfanonin kirar sassan laturoni na “Chips” na Amurka sayar da hajojin su ga kasuwannin Sin da dai saura su.

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Maimakon daukar matakan zargi, da danniya, da kariyar cinikayya da nuna son kai, kamata ya yi Amurka ta hada gwiwa da kasar Sin, da ma sauran kasashen duniya, wajen gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, ta yadda moriyar bai daya ta dukkanin sassa za ta zarce ta kashin kai. A daya bangaren kuma, nuna fuska biyu, da fada ba cikawa, ba abun da za su haifar illa raba kawuna, da gurgunta amincewa da juna, da lalata moriyar duniya baki daya.( Saminu Alhassan)

Blinken
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

MASU ALAKA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Daga Birnin Sin

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.