• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Gwamnatin Kano Da NNPP Sun Illata Siyasar Ganduje Duk Da Rashin Nasarar’

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar APC na yankin arewa maso yamma, Salihu Lukman ya bayyana cewa ko da ba a samu nasarar cire shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abudullahi Ganduje daga mukaminsa, an yi masa babban illa a siyasar a jiharsa.

Ya kara da cewa dalilin da ya sa gwamnatin Kano da magoya bayan jam’iyyar NNPP suka yi nasarar illata siyasar Ganduje shi ne, lokacin da ya zama shugaban jam’iyyar ya bar jihar tare da amintattun abokansa.
Lukman ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja mai taken “Hatsarin mummunan shugabancin APC.”

  • Hisbah Ta Ware Wa ‘Yan Jarida Gurbin Mutane 50 A Auren Gata A Kano
  • An Gurfanar Da Mutane 2 A Kotun Sojoji Kan Harin Tudun Biri

An dai kusan shafe wata guda ana yunkurin tsige Ganduje daga mukaminsa. A ranar Alhamis da ta gabata ce, masu zanga-zanga suka mamaye sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, domin neman Ganduje ya sauka daga kan mukaminsa jna shugabancin jam’iyyar, sannan a dawo wa yankin arewa ta tsakiya da mukamin wanda Abudullahi Adamu dan yankin ya rike kafin a bai wa Ganduje.

Masu zanga-zanga sun danganta bukatar ne kan dakatarwar da shugabannin mazaba Ganduje suka yi masa kan zargin amsar cin hanci da rashawa da gwamnatin Jihar Kano take yi masa.
Sai dai Lukman ya dage da cewa wannan lamari ba zai faru ba idan da a ce tsohon gwamnan bai dauke amintattun abokansa ba lokacin da ya zama shugaban jam’iyyar APC suka bar Jihar Kano.

Ya ce, “A lokacin da Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa, dukkan shugabannin APC na Jihar Kano suka dawo Abuja. Wannan yana daga cikin dalilin da ya sa gwamnatin Jihar Kano ta samu nasarar illata siyasar Ganduje, saboda rashin shuganannin APC a Kano.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

“Gaskiyar magana ita ce, tun lokacin da Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa tsawon wata tara sau biyu ya je Kano. Jam’iyyar adawa ce ke mulki a jihar kuma yana so APC ta kara kwace Kano.

“Idan har Shugaban kasa, Asiwaju Tinubu wanda yake da ayyuka da yawa zai je Jihar Legas fiye da sau biyar, tabbas abun kunya ne a ce Ganduje ya bayar da uzuri na kasa amfani da mukaminsa na shugaban jam’iyyar APC na kasa wajen tallata siyasarsa. Raunin siyasa ne ake ya samu nakasu a mahaifarsa,” in ji shi.

Haka kuma dan siyasar na Jihar Kaduna ya zargi Shugaba Tinubu kan ci gaba da mayar da yankin arewa ta tsakiya saniyar ware daga mukamin shugabancinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCNNPPSiyasar Kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sanatoci Sun Tayar Da Jijiyar Wuya Kan Tsarin Kujerun Zama A Majalisa

Next Post

Xi Ya Yi Kira Ga Matasa Da Su Dauki Nauyin Zamanantar Da Kasar Sin

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

3 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Xi Ya Yi Kira Ga Matasa Da Su Dauki Nauyin Zamanantar Da Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Matasa Da Su Dauki Nauyin Zamanantar Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.