• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tubabben Kwamandan Boko Haram Ya Bayyana Ta’asar Da Suka Tafka A Sambisa

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Boko

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Wasu daga cikin tsofaffin kwamandojin kungiyar Jama’atu Ahlussunnah lil’da’wati wal jihad da aka fi sani da Boko Haram sun bayyana nadamar irin ta’addancin da suka tafka a matsayinsu na mayakan kungiyar a baya.

Da suke tattaunawa da sashen Hausa na Muryar Amurka, daya daga cikin hadiman dake zama daya daga cikin hadiman tsohon shugaban kungiyar Abubakar Shekau, kuma daya daga cikin wadanda suka sace daliban Chibok, ya ce abin da suka yi a baya hakika bai dace ba, kuma babban abin takaici ne.

  • Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba
  • Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 5.7 A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Ya ce ya san Abubakar Shekau shekaru da dama kafin ma a fara rikicin na Arewa  maso Gabas, ko da aka ji wa shekau din rauni, an kawo shi Damaturu, inda yake jinya kuma a lokacin shike yi masa ‘yan aikace-aikace da wanki da da sauransu.

Bayan da kuma Shekau ya koma daji su kan aika masa da kudi don biyan bukatun yau da kullum kafin daga bisani shima ya bisu dajin, inda bayan samun horo, shima ya zama cikakken kwamandan dake jagorantar kai hare- hare.

Wannan tsohon kwamandan da ya ce ya jagoranci kai hare-hare a sassan Arewa maso Gabas da dama, ya yi ikirarin kashe fararen hula da sojojin da bai san adadinsu ba, al’amarin kuma da ya ce yana matukar bakin cikin hakan.

Bugu da kari, ya kuma yi bayanin yadda ya taka rawa yayin sace daliban Chibok inda suka kai su dajin Sambisa, koda yake ya ce shi bai auri ko daya ba, amma abokansa da dama sun aure su.

Ya ce babban abin da ya sa ya fice daga kungiyar ta’addancin shi ne yadda ake sa su karkashe mutane wasu ma ta hanyar yankan rago ba gaira ba dalili.

Da kuma yake amsa tambayar ko ina Leah Sheribu take? daliba zaya tilo daga cikin daliban Dapchi da ta rage a hanun yan ta’addan, wannan tubabben kwamandan na Boko Haram ya ce LEAH tana hanun mayakan Boko Haram tsagin ISWAP a yankin tafkin Tchadi.

Ya ce abokansu ne ke rike da ita, kuma sun mata aure har ta haifi yara biyu, namiji da mace, koda yake mijinta na farko ya rasu, amma wani dan ta’addan ya sake aure ta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Kotu Ta Aike Da Ramlat Princess Zuwa Gidan Gyaran Hali Na Kano Tsawon Watanni Bakwai

Gwamnatin Kano Ta Biya Wa Ɗalibai 1,740 Kuɗin Makaranta A Jami'ar Ilimi Ta Sa'adatu Rimi

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.