• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (8)

Ci gaba daga makon jiya

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Tarihi
0
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (8)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau daya daga cikin wadancan wurare mai suna Abuja ta zama abin alfari ga kasar Nijeriya baki daya, inda ta zama abin tunkahon jama’ar Nijeriya a matsayin Gundumar mulkin kasa baki daya.

An amshi wannan wuri (Abuja) a hannun Sarki Sulaimanu Barau a matsayin gundumar mulkin kasa a shekara ta 1976.

  • Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?
  • Nijeriya Na Kara Kaimin Bunkasa Sufurin Jiragen Sama Ta Hanyar Fasahar Tauraron Dan’adam – Keyamo

A nan zamu iya ganin yadda aikin Sarki mai adalci Muhammadu Makau dan Sarki Isyaku Jatau ya kai. Wannan ba karamin abin alfahari ne ba.

Zazzagawan dauri wato na da can sun ci gaba da huddarsu da Fulani da ke makwabtaka da su,masu  zama a Bida. Amma jama’ar da ke kasar Zariya sun komo da hujja da sabuwar kasar Muhammadu Makau dole a zamanin Sarki Abubakar Kwakwa, daga shekara ta 1851 zuwa 1877.

Fadar sarki

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

Wannan ya faru a dalilin tsaida duk wani nau’in kasuwanci tsakanin kasar da kudancin Nijeriya.

Bayanan abubuwan da suka wakana a tsakanin ma su da’awar karbar tuta daga hannun Shehu Usmanu na tattare a gun wadanda abin ya shafa,inda za ka iya samun gaskiyar abin da ya gudana a tsakaninsu. Amma ga al’amarin Hausa-Fulani ba za su tsaya su tsage gaskiya don kowa ya ganta ba, illa su bayyana cewar sun kori kafurai ko su yi amfani da kalmar maguzanci.Allah mai girma, in muka ce za mu yi maganar irin nau’in mulkin da suka yi wa jama’a tabbas mutunci da kimatsu za su zuba a idon jama’a musamman ‘yan bana-bakwai. Domin in aka fassara kalmar Maguzanci kuma aka duba ta daya bayan daya zamu ga irin mummunar zaman da aka yi ko ince a ke yi da su, in da hatta su kansu ba su bar junan su ba. Bari mu ga wani abu daga cikin al’amurran da suka faru a yake-yaken jihadi ko son mulki sun ci gaba da gudana kuma jama’a sun ci gaba da hijira daga wannan wuri zuwa wancan wuri har ya zuwa shekara ta 1808 inda Fulani suka kama yammacin Ngazargamu wanda yake shi ne birnin daular Borno. Amma daga karshe a cikin shekara ta 1809 Sheikh Lamido ya kori Hausa-Fulani daga daular Borno.

Masarautar Zazzau

Babbar kofar shiga masarautar Zazzau da ke Zariya

Zazzau ko Zariya Masarauta ce t mai dadadden Tarihi ta Hausawa wadda ta ke da gidan sarautar ta a birnin Zariya a jihar Kaduna a Arewacin Najeriya . Alhaji Shehu Idris Shine Sarkin Zazzau a wancan lokacin.

Maguzanci

Abu mafi mahimman ci da zamu fara dubawa wajen gane tarihin masarautar Zazzau shine labarun da suka shahara a karni na ashirin. Wanda yake nuna cewa asalin kafuwar masarautun Hausa abin ya fara ne daga kanen Bayajidda,Wato wani Jarumi da ake fada a tarihin Hausawa wanda shine asalin kafuwar masarautun Hausa da muke da su a wannan zamanin.Kamar yadda masana Tarihi suke fada cewa a karni na goma sha daya ne aka kafa masarautar zazzau bisa jogorancin Sarkin Zazzau Gunguma.Daga nanne kuma aka kafa masarautar Zazzau ta zama daya daga cikin masarautun Hausawa ko Habe na Hausa Bakwai.Fitacciyar wadda tayi iko a masarautar Zazzau it ace Sarauniyar Zazzau Amina.

Wacce tayi iko ko dai tsakiyar karni na sha biyar ko kuma tsakiyar karni na sha shida. Birnin Zazzau ya zama cibiyar harhada bayi inda ake cinikin su zuwa Arewacin Najeriya kamar birnin Kano da birnin Katsina inda ake kasuwancin Bayi ta hanyar kasuwancin ban gishiri na baka Manda daga nan kuma sai a wuce da Bayin zuwa Sahara.A yadda tarihi yazo Musulunci ya shiga Masarautar Zazzau ne a wajen shekara ta 1456 amma kadan daga cikin wasu mutanen na ci gaba da tsafi yayin da wadansu kuma ke Maguzanci Har zuwa lokacin da jihadin Shehu Usman Dan fodiyo ya zo a shekarar 1808. Ayanzu dai Masarautar Zazzau Masarauta ce da ta yi kaurin suna wajen tafiyar da Addinin Musulunci.Akwai manya manyan malamai na Musulunci a Masarautar.

Sarautar Fulani a Masarautar Zazzau

A watan Disamba na 1808 Mujahidai karkashin Jahorancin Mujadda Shehu Usman Danfodiyo suka samu nasarar korar Masu rike da sarautar lokacin wadanda Habe ne ko Hausawa.Hakanne yasa su Hausawan suka gudu zuwa yankin Abuja Suka tare a wajen da ake kira Suleja a yanzu.Shi yasa har yanzu ake kiran sarautar ko kuma sarkin Suleja da Sarkin Zazzau. Tarihin Bayajidda wanda a yau masana na kallonsa a kagaggen labari domin tambayoyin da ke kansa sun kasa amsuwa. Amma in muka kalli manufa ta wannan labari zamu ga cewar an samar da shi ne don samar da zaman lafiya tsakanin kasashen Hausa.In muka kalla ta bangaren nazartar harshe zamu ga wannan tarihi bai da hurumin ko kusa musamman in muka kalli kalmomi da ke rataye da kasar Zazzau.

An samo wannan  Tarihin ne daga encyclopedia ta Hausa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Masarautar ZazzauTarihi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalolin Gidan Aure Da Yadda Za A Gyara (1)

Next Post

Gyaran Jiki A Saukake

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da É—umi-É—uminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

4 days ago
majalisar kasa
Tarihi

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

1 week ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

1 month ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

2 months ago
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
Tarihi

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

3 months ago
Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

5 months ago
Next Post
Gyaran Jiki A Saukake

Gyaran Jiki A Saukake

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da ÆŠangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da ÆŠangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Zazzau

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.