ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (8)

Ci gaba daga makon jiya

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Zazzau

A yau daya daga cikin wadancan wurare mai suna Abuja ta zama abin alfari ga kasar Nijeriya baki daya, inda ta zama abin tunkahon jama’ar Nijeriya a matsayin Gundumar mulkin kasa baki daya.

An amshi wannan wuri (Abuja) a hannun Sarki Sulaimanu Barau a matsayin gundumar mulkin kasa a shekara ta 1976.

  • Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?
  • Nijeriya Na Kara Kaimin Bunkasa Sufurin Jiragen Sama Ta Hanyar Fasahar Tauraron Dan’adam – Keyamo

A nan zamu iya ganin yadda aikin Sarki mai adalci Muhammadu Makau dan Sarki Isyaku Jatau ya kai. Wannan ba karamin abin alfahari ne ba.

ADVERTISEMENT

Zazzagawan dauri wato na da can sun ci gaba da huddarsu da Fulani da ke makwabtaka da su,masu  zama a Bida. Amma jama’ar da ke kasar Zariya sun komo da hujja da sabuwar kasar Muhammadu Makau dole a zamanin Sarki Abubakar Kwakwa, daga shekara ta 1851 zuwa 1877.

Fadar sarki

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Wannan ya faru a dalilin tsaida duk wani nau’in kasuwanci tsakanin kasar da kudancin Nijeriya.

Bayanan abubuwan da suka wakana a tsakanin ma su da’awar karbar tuta daga hannun Shehu Usmanu na tattare a gun wadanda abin ya shafa,inda za ka iya samun gaskiyar abin da ya gudana a tsakaninsu. Amma ga al’amarin Hausa-Fulani ba za su tsaya su tsage gaskiya don kowa ya ganta ba, illa su bayyana cewar sun kori kafurai ko su yi amfani da kalmar maguzanci.Allah mai girma, in muka ce za mu yi maganar irin nau’in mulkin da suka yi wa jama’a tabbas mutunci da kimatsu za su zuba a idon jama’a musamman ‘yan bana-bakwai. Domin in aka fassara kalmar Maguzanci kuma aka duba ta daya bayan daya zamu ga irin mummunar zaman da aka yi ko ince a ke yi da su, in da hatta su kansu ba su bar junan su ba. Bari mu ga wani abu daga cikin al’amurran da suka faru a yake-yaken jihadi ko son mulki sun ci gaba da gudana kuma jama’a sun ci gaba da hijira daga wannan wuri zuwa wancan wuri har ya zuwa shekara ta 1808 inda Fulani suka kama yammacin Ngazargamu wanda yake shi ne birnin daular Borno. Amma daga karshe a cikin shekara ta 1809 Sheikh Lamido ya kori Hausa-Fulani daga daular Borno.

Masarautar Zazzau

Babbar kofar shiga masarautar Zazzau da ke Zariya

Zazzau ko Zariya Masarauta ce t mai dadadden Tarihi ta Hausawa wadda ta ke da gidan sarautar ta a birnin Zariya a jihar Kaduna a Arewacin Najeriya . Alhaji Shehu Idris Shine Sarkin Zazzau a wancan lokacin.

Maguzanci

Abu mafi mahimman ci da zamu fara dubawa wajen gane tarihin masarautar Zazzau shine labarun da suka shahara a karni na ashirin. Wanda yake nuna cewa asalin kafuwar masarautun Hausa abin ya fara ne daga kanen Bayajidda,Wato wani Jarumi da ake fada a tarihin Hausawa wanda shine asalin kafuwar masarautun Hausa da muke da su a wannan zamanin.Kamar yadda masana Tarihi suke fada cewa a karni na goma sha daya ne aka kafa masarautar zazzau bisa jogorancin Sarkin Zazzau Gunguma.Daga nanne kuma aka kafa masarautar Zazzau ta zama daya daga cikin masarautun Hausawa ko Habe na Hausa Bakwai.Fitacciyar wadda tayi iko a masarautar Zazzau it ace Sarauniyar Zazzau Amina.

Wacce tayi iko ko dai tsakiyar karni na sha biyar ko kuma tsakiyar karni na sha shida. Birnin Zazzau ya zama cibiyar harhada bayi inda ake cinikin su zuwa Arewacin Najeriya kamar birnin Kano da birnin Katsina inda ake kasuwancin Bayi ta hanyar kasuwancin ban gishiri na baka Manda daga nan kuma sai a wuce da Bayin zuwa Sahara.A yadda tarihi yazo Musulunci ya shiga Masarautar Zazzau ne a wajen shekara ta 1456 amma kadan daga cikin wasu mutanen na ci gaba da tsafi yayin da wadansu kuma ke Maguzanci Har zuwa lokacin da jihadin Shehu Usman Dan fodiyo ya zo a shekarar 1808. Ayanzu dai Masarautar Zazzau Masarauta ce da ta yi kaurin suna wajen tafiyar da Addinin Musulunci.Akwai manya manyan malamai na Musulunci a Masarautar.

Sarautar Fulani a Masarautar Zazzau

A watan Disamba na 1808 Mujahidai karkashin Jahorancin Mujadda Shehu Usman Danfodiyo suka samu nasarar korar Masu rike da sarautar lokacin wadanda Habe ne ko Hausawa.Hakanne yasa su Hausawan suka gudu zuwa yankin Abuja Suka tare a wajen da ake kira Suleja a yanzu.Shi yasa har yanzu ake kiran sarautar ko kuma sarkin Suleja da Sarkin Zazzau. Tarihin Bayajidda wanda a yau masana na kallonsa a kagaggen labari domin tambayoyin da ke kansa sun kasa amsuwa. Amma in muka kalli manufa ta wannan labari zamu ga cewar an samar da shi ne don samar da zaman lafiya tsakanin kasashen Hausa.In muka kalla ta bangaren nazartar harshe zamu ga wannan tarihi bai da hurumin ko kusa musamman in muka kalli kalmomi da ke rataye da kasar Zazzau.

An samo wannan  Tarihin ne daga encyclopedia ta Hausa

Zazzau
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Gyaran Jiki A Saukake

Gyaran Jiki A Saukake

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.