• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zangar Karin Kudin Wuta: Gwamnati Ta Shelanta Matakin Da Za Ta Dauka

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Zanga-zangar Karin Kudin Wuta: Gwamnati Ta Shelanta Matakin Da Za Ta Dauka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan tirjiya na karin kudin wutan lantarki da hukumomi suka yi a Nijeriya a watan da ta gabata, kungiyar kwadago a Nijeriya sun dukufa wajen gudanar da zanga-zanga tare da neman dole a canye zancen karin kudin wuta da kuma magance matsalar wutar lantarki.

Rahotonni sun yi nuni da cewa kungiyar kwadago sun rufe dukkanin ofisoshin kamfanonin rarraba wutar lantaki guda 11 da babban ofishin hukumar kula da wutar lantarki ta kasa a yayin da suka tsunduma gudanar da zanga-zangar na ranar Litinin.

  • Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi
  • Za A Bude Shafin Karbar Bashin Dalibai A Ranar 24 Ga Mayu

Shugaban kungiyar kwadago, Joe Ajaero shi ne ya jagoranci zanga-zangar a Abuja har zuwa ga ministan wuta da kuma shalkwatar hukumar kula da lamarin wuta a Nijeriya (NERC).

 Sannan an rufe ofishin kamfanin rarraba wutar lantarki tare da hana ma’aikata shiga domin gudanar da aiki.

 Bugu da kari, haka zancen yake a sauran ofisoshin kamfanin da ke jihohi da suka hada da na Kwara, Legas, Kaduna, Filato, Inugu, Sakkwato, Bauchi da sauran ofisoshi da suke sassan kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Ajaero, yayin zanga-zangar, ya ce akwai bukatar NERC ta sake nazarin matakan da suka bi wajen karin kudin wuta. Ya ce, karin kudin ya janyo tashin farashin ababe da dama musamman kayan abinci.

 A martaninta kan zanga-zangar na kwana guda, gwamnatin Nijeriya ta ce ta fara tattaunawa da kungiyar kwadago kan lamarin.

Kakakin ministan wuta a Nijeriya, Florence Eke, ta shaida wa majiyarmu ta wayar tarho cewa bayan zanga-zangar ma’aikatan, gwamnatin tarayya ta hannun babban sakatare, Mista Mamman Mahmuda, ya kira taron ganawa da kungiyar kwadago a mako mai zuwa, ganawar da zai hada har da masu ruwa da tsaki domin lalubo bakin zaren matsalar.

“Ma’aikatar wuta za ta gayyaci dukkanin masu ruwa da tsaki domin nemo mafita kan wannan batun a mako mai zuwa,” ta shaida.

Mai magana da yawun kungiyar kwadago, Benson Upah, ya ce, ya kamata ne gwamnati ta tuntubi masu ruwa da tsaki tun kafin ta aiwatar da manufar karin kudin wutar a ranar 3 ga watan Afrilu.

Ya tabbatar da cewa zanga-zanga da suka fara muddin gwamnati ta kasa komawa baya kan matakinta na karin kudin lantarki za su ci gaba.

Idan za a tuna dai a watan Afrilun 2024 ne hukumar kula da wutar lantarki a Nijeriya ta sanar da karin kudin lantarki da kaso 240 ga kwastomomin da ke amfani da rukunin A.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiKarin Kudin WutaLantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Philippines Da Ta Dakatar Da Tada Zaune Tsaye A Yankin Tekun Kudancin Sin

Next Post

Yadda Sin Da Rasha Suke Mu’amala Da Juna Ya Samar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

14 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

18 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

19 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

20 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

22 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

1 day ago
Next Post
Yadda Sin Da Rasha Suke Mu’amala Da Juna Ya Samar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Yadda Sin Da Rasha Suke Mu’amala Da Juna Ya Samar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.