• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Ce Kirkirarriyar Basira ‘AI’ Za Ta Taimaka Wajen Kare Makarantu

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Minista Ya Ce Kirkirarriyar Basira ‘AI’ Za Ta Taimaka Wajen Kare Makarantu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karamin Ministan Ilimi, Dakta Yusuf Tanko Sununu, ya jaddada cewa amfani da kirkirarriyar basira (Artificial Intelligence) zai bunkasa da kyautata fasahohin da ake da su a bangaren koyarwa da tsaron makarantu.

Wanda ke magana a wajen taron kwararru kan fasahar sadarwar zamani na 2024 karo na goma sha takwas da ya gudana a Abuja.
A cewarsa, “Amfani da basirar AI a dukkanin makarantunmu zai taimaka mana wajen koyarwa, bibiya da kuma tabbatar da makarantunmu suna cikin tsaro.”

  • Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand
  • Ana Samun Saukin Yaduwar Bakuwar Cutar Da Ta Barke A Zamfara

Ya ce, akwai gayar bukatar amfani da fasahohin zamani ciki kuwa har da na AI wajen karfafa wa sintiri da sanya ido kan muhallan makarantu, a cewarsa, “Ya zama dole a garemu mu rungumi yadda za mu tafiya da fasahohi, ciki har da na AI wajen aza tubalin bibiya da ayyukan sirri na tsawo da za su kaimu ga kare makarantunmu.”

Ya nemi taron kwararrun da cewa zai bullo da wasu hanyoyi da shawarorin yadda za su taimaka wa gwamnati wajen zuba na’urorin zamani kuma a tabbatar da sun yi aiki bisa hadin guiwa domin kyautata tattalin arziki, matakin fasaha, da wayar da kai kan tsaron kasar nan.

“Mun gani kuma muna kan ganin alfanu da fa’idar fasahar sadarwar zamani (IT) a karni na 21 da kuma irin rawar da take takawa wajen kyautata tattalin arzikin duniya.
“Mun kuma gano irin tasirin da take da shi wajen fadadawa da saukaka hanyoyin samun ilimi a dukkanin matakai,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Ministan ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya a shirye take ta bi dukkanin matakan da suka dace wajen amfani da fasaha don ganin an samu nasarar bunkasa cigaba da rungumar fasahar sadarwar zamani a tsarin ilimin Nijeriya.

“Gwamnatin tarayya ta dukufa wajen ganin ta kai Nijeriya da ajiyeta a matsayin shugaba a duniya, musamman a Afrika. Bangaren fasahar sadarwar zamani na taka muhimmiyar rawa wajen cimma wannan manufar da gwamnati ta sanya a gaba,” Sununu ya shaida.

Ya bukaci kwararrun da su mara wa yunkuri da shirin gwamnati baya gami da bada nasu gudunmawar domin cigaba da daurewar tattalin arzikin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Hannun Nuhu Ribaɗo Wajen Yunƙurin Dawo Da Aminu Ado Sarauta

Next Post

Hukumomin Tsaro A Kano Sun Ƙi Biyayya Ga Umarnin Gwamnan Kano

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

4 hours ago
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa
Labarai

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

6 hours ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

9 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanaki 10 A Faransa Da Birtaniya

9 hours ago
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Manyan Labarai

Gargaɗi: Ƙauyuka 43 A Jihohi 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa 

11 hours ago
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci
Labarai

Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

12 hours ago
Next Post
Hukumomin Tsaro A Kano Sun Ƙi Biyayya Ga Umarnin Gwamnan Kano

Hukumomin Tsaro A Kano Sun Ƙi Biyayya Ga Umarnin Gwamnan Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

September 4, 2025
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

September 4, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

September 4, 2025
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.