• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Ce Kirkirarriyar Basira ‘AI’ Za Ta Taimaka Wajen Kare Makarantu

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Minista

Karamin Ministan Ilimi, Dakta Yusuf Tanko Sununu, ya jaddada cewa amfani da kirkirarriyar basira (Artificial Intelligence) zai bunkasa da kyautata fasahohin da ake da su a bangaren koyarwa da tsaron makarantu.

Wanda ke magana a wajen taron kwararru kan fasahar sadarwar zamani na 2024 karo na goma sha takwas da ya gudana a Abuja.
A cewarsa, “Amfani da basirar AI a dukkanin makarantunmu zai taimaka mana wajen koyarwa, bibiya da kuma tabbatar da makarantunmu suna cikin tsaro.”

  • Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand
  • Ana Samun Saukin Yaduwar Bakuwar Cutar Da Ta Barke A Zamfara

Ya ce, akwai gayar bukatar amfani da fasahohin zamani ciki kuwa har da na AI wajen karfafa wa sintiri da sanya ido kan muhallan makarantu, a cewarsa, “Ya zama dole a garemu mu rungumi yadda za mu tafiya da fasahohi, ciki har da na AI wajen aza tubalin bibiya da ayyukan sirri na tsawo da za su kaimu ga kare makarantunmu.”

Ya nemi taron kwararrun da cewa zai bullo da wasu hanyoyi da shawarorin yadda za su taimaka wa gwamnati wajen zuba na’urorin zamani kuma a tabbatar da sun yi aiki bisa hadin guiwa domin kyautata tattalin arziki, matakin fasaha, da wayar da kai kan tsaron kasar nan.

“Mun gani kuma muna kan ganin alfanu da fa’idar fasahar sadarwar zamani (IT) a karni na 21 da kuma irin rawar da take takawa wajen kyautata tattalin arzikin duniya.
“Mun kuma gano irin tasirin da take da shi wajen fadadawa da saukaka hanyoyin samun ilimi a dukkanin matakai,” ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Ministan ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya a shirye take ta bi dukkanin matakan da suka dace wajen amfani da fasaha don ganin an samu nasarar bunkasa cigaba da rungumar fasahar sadarwar zamani a tsarin ilimin Nijeriya.

“Gwamnatin tarayya ta dukufa wajen ganin ta kai Nijeriya da ajiyeta a matsayin shugaba a duniya, musamman a Afrika. Bangaren fasahar sadarwar zamani na taka muhimmiyar rawa wajen cimma wannan manufar da gwamnati ta sanya a gaba,” Sununu ya shaida.

Ya bukaci kwararrun da su mara wa yunkuri da shirin gwamnati baya gami da bada nasu gudunmawar domin cigaba da daurewar tattalin arzikin kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
Hukumomin Tsaro A Kano Sun Ƙi Biyayya Ga Umarnin Gwamnan Kano

Hukumomin Tsaro A Kano Sun Ƙi Biyayya Ga Umarnin Gwamnan Kano

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.