ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand

by Abubakar Abba
2 years ago
Shinkafa

Fargaba da damuwa na kara karuwa, sakamakon rade-radin da ake yi na shigo da Shinkafa daga Kasar Thailand zuwa Nijeriya, don sayar da ita; wadda ake zargin ta jima a ajiye har tsawon shekara goma ba tare da an yi amfani da ita.

Wannan fargabar dai, ta biyo bayan wata sanawar ce; wadda Gwamnatin Kasar Thailand ta sanar cewa, za ta tura wannan Shinkafar zuwa Kasashen Nahiyar Afirkar; domin sayarwa.

  • Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga
  • Zamba Ba Za Ta Yaudari Al’ummomin Kasa Da Kasa Ba

Gwamnatin kasar na shirin yin gwanjon buhunhunan Shinkafar ne guda 150,000, wadda ta ajiye su a runbunanta na ajiya, har tsawon shekaru goma.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, kasar ta Thailand na sa ran sama wa da kanta kudin shiga ne ta hanayr sayar da wannan Shinkafa, domin kuwa yawan kudin ya kai kimamin daga Baht miliyan 200 zuwa 400 na kudin kasar, inda kudin ya kai Dala miliyan 5.4 zuwa 10.8.

Tun bayan da gwamnatin ta Thailand ta bayyana wannan shiri nata ne, wasu masana da wasu ‘yan Nijeriya a shafukan sada zumunta na zamani, suka fara yin mummunar suka a kan wannan shirin na gwamnatin Thailand na turo da wadannan buhunhunan Shinkafar zuwa Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Sun yi sukar ne, duba da yadda yin amfani da Shinkafar zai shafi kiwon lafiyar al’ummar wannan kasa; idan har aka shigo da ita Nijeriya, musamman ganin yadda ba a dauki wasu kwararan matakan da ke sanyo ido a kan ingancin kayan da ake shigowa da su cikin kasar ba.

Wani dan Nijeriya mai suna NwaOnyekuzi, ya wallafa nasa bacin ran a kafarsa ta Di (Tweeter), inda ya ce; wannan shiri na gwamnatin Thailand, cin mutuci ne ga ita kanta Nijeriya.

Bugu da kari, wata kididdiga ta nuwa cewa; daga kakar 2023 zuwa 2024, Kasar Thailand ta kasance ta biyu da ke a kan gaba a fadin duniya wajen safarar Shinkafar da ta kai tan miliyan 8.2.

Wani kwararre a fannin samar da ingantaccen abinci, mai suna James Marsh ya sanar da cewa, wannan Shinkafa wadda ta shafe shekaru goma a ajiye a cikin rumbunan Thailand, sakamakon dadewar da ta yi babu wani sinadari mai gina jikin Dan’adam da za a mora daga cikinta.

A cewarsa, saboda yawan feshen da aka yi mata don kare ta daga lalacewa, zai iya shafar kiwon lafiyar duk wanda ya yi amfani da ita.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa, a ka’ida ba a son buhunhunan Shinkafar da aka adana cikin rumbu su wuce tsawon shekaru biyar a ajiye.

Sannan, ya nuna takaicinsa kan cewa; wadannan buhunhunan Shinkafar, za su samu hanyar shigowa cikin kasar nan duba da yanayin da iyakokin Nijeriya suka kasance.

Ya kuma shawarci gwamnatin tarayya cikin gaggawa ta dauki matakan da suka dace, domin dakile shigo da wannan Shinkafa cikin wannan kasa, inda ya kara da cewa; wannan babban aiki ne a gaban hukumominmu.
Har ila yau, ya sanar da cewa; wannan Shinkafa na dauke da lamba wadda za a iya saurin gane ta.

Shi ma wani kwarrre a fannin kimiyyar abinci da ke Jami’ar Aikin Noma ta Tarayya, Farfesa Shittu Akinyemi ya sanar da cewa, kula da ingancin abinci ya kasu kashi biyu ne, wato yadda aka lula da shi da kuma irin magungunan feshin da aka zuba wa hatsin don kare shi daga kwari.

A cewarsa, ana iya adana hatsi har zuwa dogon zango, sai dai; mutane na jin tsoro kan yadda aka ajiye kayan abinci har zuwa tsawon lokaci, musamman ma Shinkafa.

Shinkafa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Sarki Biyu A Gari Ɗaya: Aminu Ado Ya Isa Kano

Sarki Biyu A Gari Ɗaya: Aminu Ado Ya Isa Kano

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.