ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand

by Abubakar Abba
2 years ago
Shinkafa

Fargaba da damuwa na kara karuwa, sakamakon rade-radin da ake yi na shigo da Shinkafa daga Kasar Thailand zuwa Nijeriya, don sayar da ita; wadda ake zargin ta jima a ajiye har tsawon shekara goma ba tare da an yi amfani da ita.

Wannan fargabar dai, ta biyo bayan wata sanawar ce; wadda Gwamnatin Kasar Thailand ta sanar cewa, za ta tura wannan Shinkafar zuwa Kasashen Nahiyar Afirkar; domin sayarwa.

  • Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga
  • Zamba Ba Za Ta Yaudari Al’ummomin Kasa Da Kasa Ba

Gwamnatin kasar na shirin yin gwanjon buhunhunan Shinkafar ne guda 150,000, wadda ta ajiye su a runbunanta na ajiya, har tsawon shekaru goma.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, kasar ta Thailand na sa ran sama wa da kanta kudin shiga ne ta hanayr sayar da wannan Shinkafa, domin kuwa yawan kudin ya kai kimamin daga Baht miliyan 200 zuwa 400 na kudin kasar, inda kudin ya kai Dala miliyan 5.4 zuwa 10.8.

Tun bayan da gwamnatin ta Thailand ta bayyana wannan shiri nata ne, wasu masana da wasu ‘yan Nijeriya a shafukan sada zumunta na zamani, suka fara yin mummunar suka a kan wannan shirin na gwamnatin Thailand na turo da wadannan buhunhunan Shinkafar zuwa Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Sun yi sukar ne, duba da yadda yin amfani da Shinkafar zai shafi kiwon lafiyar al’ummar wannan kasa; idan har aka shigo da ita Nijeriya, musamman ganin yadda ba a dauki wasu kwararan matakan da ke sanyo ido a kan ingancin kayan da ake shigowa da su cikin kasar ba.

Wani dan Nijeriya mai suna NwaOnyekuzi, ya wallafa nasa bacin ran a kafarsa ta Di (Tweeter), inda ya ce; wannan shiri na gwamnatin Thailand, cin mutuci ne ga ita kanta Nijeriya.

Bugu da kari, wata kididdiga ta nuwa cewa; daga kakar 2023 zuwa 2024, Kasar Thailand ta kasance ta biyu da ke a kan gaba a fadin duniya wajen safarar Shinkafar da ta kai tan miliyan 8.2.

Wani kwararre a fannin samar da ingantaccen abinci, mai suna James Marsh ya sanar da cewa, wannan Shinkafa wadda ta shafe shekaru goma a ajiye a cikin rumbunan Thailand, sakamakon dadewar da ta yi babu wani sinadari mai gina jikin Dan’adam da za a mora daga cikinta.

A cewarsa, saboda yawan feshen da aka yi mata don kare ta daga lalacewa, zai iya shafar kiwon lafiyar duk wanda ya yi amfani da ita.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa, a ka’ida ba a son buhunhunan Shinkafar da aka adana cikin rumbu su wuce tsawon shekaru biyar a ajiye.

Sannan, ya nuna takaicinsa kan cewa; wadannan buhunhunan Shinkafar, za su samu hanyar shigowa cikin kasar nan duba da yanayin da iyakokin Nijeriya suka kasance.

Ya kuma shawarci gwamnatin tarayya cikin gaggawa ta dauki matakan da suka dace, domin dakile shigo da wannan Shinkafa cikin wannan kasa, inda ya kara da cewa; wannan babban aiki ne a gaban hukumominmu.
Har ila yau, ya sanar da cewa; wannan Shinkafa na dauke da lamba wadda za a iya saurin gane ta.

Shi ma wani kwarrre a fannin kimiyyar abinci da ke Jami’ar Aikin Noma ta Tarayya, Farfesa Shittu Akinyemi ya sanar da cewa, kula da ingancin abinci ya kasu kashi biyu ne, wato yadda aka lula da shi da kuma irin magungunan feshin da aka zuba wa hatsin don kare shi daga kwari.

A cewarsa, ana iya adana hatsi har zuwa dogon zango, sai dai; mutane na jin tsoro kan yadda aka ajiye kayan abinci har zuwa tsawon lokaci, musamman ma Shinkafa.

Shinkafa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Sarki Biyu A Gari Ɗaya: Aminu Ado Ya Isa Kano

Sarki Biyu A Gari Ɗaya: Aminu Ado Ya Isa Kano

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.