ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand

by Abubakar Abba
2 years ago
Shinkafa

Fargaba da damuwa na kara karuwa, sakamakon rade-radin da ake yi na shigo da Shinkafa daga Kasar Thailand zuwa Nijeriya, don sayar da ita; wadda ake zargin ta jima a ajiye har tsawon shekara goma ba tare da an yi amfani da ita.

Wannan fargabar dai, ta biyo bayan wata sanawar ce; wadda Gwamnatin Kasar Thailand ta sanar cewa, za ta tura wannan Shinkafar zuwa Kasashen Nahiyar Afirkar; domin sayarwa.

  • Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga
  • Zamba Ba Za Ta Yaudari Al’ummomin Kasa Da Kasa Ba

Gwamnatin kasar na shirin yin gwanjon buhunhunan Shinkafar ne guda 150,000, wadda ta ajiye su a runbunanta na ajiya, har tsawon shekaru goma.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, kasar ta Thailand na sa ran sama wa da kanta kudin shiga ne ta hanayr sayar da wannan Shinkafa, domin kuwa yawan kudin ya kai kimamin daga Baht miliyan 200 zuwa 400 na kudin kasar, inda kudin ya kai Dala miliyan 5.4 zuwa 10.8.

Tun bayan da gwamnatin ta Thailand ta bayyana wannan shiri nata ne, wasu masana da wasu ‘yan Nijeriya a shafukan sada zumunta na zamani, suka fara yin mummunar suka a kan wannan shirin na gwamnatin Thailand na turo da wadannan buhunhunan Shinkafar zuwa Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Sun yi sukar ne, duba da yadda yin amfani da Shinkafar zai shafi kiwon lafiyar al’ummar wannan kasa; idan har aka shigo da ita Nijeriya, musamman ganin yadda ba a dauki wasu kwararan matakan da ke sanyo ido a kan ingancin kayan da ake shigowa da su cikin kasar ba.

Wani dan Nijeriya mai suna NwaOnyekuzi, ya wallafa nasa bacin ran a kafarsa ta Di (Tweeter), inda ya ce; wannan shiri na gwamnatin Thailand, cin mutuci ne ga ita kanta Nijeriya.

Bugu da kari, wata kididdiga ta nuwa cewa; daga kakar 2023 zuwa 2024, Kasar Thailand ta kasance ta biyu da ke a kan gaba a fadin duniya wajen safarar Shinkafar da ta kai tan miliyan 8.2.

Wani kwararre a fannin samar da ingantaccen abinci, mai suna James Marsh ya sanar da cewa, wannan Shinkafa wadda ta shafe shekaru goma a ajiye a cikin rumbunan Thailand, sakamakon dadewar da ta yi babu wani sinadari mai gina jikin Dan’adam da za a mora daga cikinta.

A cewarsa, saboda yawan feshen da aka yi mata don kare ta daga lalacewa, zai iya shafar kiwon lafiyar duk wanda ya yi amfani da ita.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa, a ka’ida ba a son buhunhunan Shinkafar da aka adana cikin rumbu su wuce tsawon shekaru biyar a ajiye.

Sannan, ya nuna takaicinsa kan cewa; wadannan buhunhunan Shinkafar, za su samu hanyar shigowa cikin kasar nan duba da yanayin da iyakokin Nijeriya suka kasance.

Ya kuma shawarci gwamnatin tarayya cikin gaggawa ta dauki matakan da suka dace, domin dakile shigo da wannan Shinkafa cikin wannan kasa, inda ya kara da cewa; wannan babban aiki ne a gaban hukumominmu.
Har ila yau, ya sanar da cewa; wannan Shinkafa na dauke da lamba wadda za a iya saurin gane ta.

Shi ma wani kwarrre a fannin kimiyyar abinci da ke Jami’ar Aikin Noma ta Tarayya, Farfesa Shittu Akinyemi ya sanar da cewa, kula da ingancin abinci ya kasu kashi biyu ne, wato yadda aka lula da shi da kuma irin magungunan feshin da aka zuba wa hatsin don kare shi daga kwari.

A cewarsa, ana iya adana hatsi har zuwa dogon zango, sai dai; mutane na jin tsoro kan yadda aka ajiye kayan abinci har zuwa tsawon lokaci, musamman ma Shinkafa.

Shinkafa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Sarki Biyu A Gari Ɗaya: Aminu Ado Ya Isa Kano

Sarki Biyu A Gari Ɗaya: Aminu Ado Ya Isa Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.