ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand

by Abubakar Abba
2 years ago
Shinkafa

Fargaba da damuwa na kara karuwa, sakamakon rade-radin da ake yi na shigo da Shinkafa daga Kasar Thailand zuwa Nijeriya, don sayar da ita; wadda ake zargin ta jima a ajiye har tsawon shekara goma ba tare da an yi amfani da ita.

Wannan fargabar dai, ta biyo bayan wata sanawar ce; wadda Gwamnatin Kasar Thailand ta sanar cewa, za ta tura wannan Shinkafar zuwa Kasashen Nahiyar Afirkar; domin sayarwa.

  • Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga
  • Zamba Ba Za Ta Yaudari Al’ummomin Kasa Da Kasa Ba

Gwamnatin kasar na shirin yin gwanjon buhunhunan Shinkafar ne guda 150,000, wadda ta ajiye su a runbunanta na ajiya, har tsawon shekaru goma.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, kasar ta Thailand na sa ran sama wa da kanta kudin shiga ne ta hanayr sayar da wannan Shinkafa, domin kuwa yawan kudin ya kai kimamin daga Baht miliyan 200 zuwa 400 na kudin kasar, inda kudin ya kai Dala miliyan 5.4 zuwa 10.8.

Tun bayan da gwamnatin ta Thailand ta bayyana wannan shiri nata ne, wasu masana da wasu ‘yan Nijeriya a shafukan sada zumunta na zamani, suka fara yin mummunar suka a kan wannan shirin na gwamnatin Thailand na turo da wadannan buhunhunan Shinkafar zuwa Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Sun yi sukar ne, duba da yadda yin amfani da Shinkafar zai shafi kiwon lafiyar al’ummar wannan kasa; idan har aka shigo da ita Nijeriya, musamman ganin yadda ba a dauki wasu kwararan matakan da ke sanyo ido a kan ingancin kayan da ake shigowa da su cikin kasar ba.

Wani dan Nijeriya mai suna NwaOnyekuzi, ya wallafa nasa bacin ran a kafarsa ta Di (Tweeter), inda ya ce; wannan shiri na gwamnatin Thailand, cin mutuci ne ga ita kanta Nijeriya.

Bugu da kari, wata kididdiga ta nuwa cewa; daga kakar 2023 zuwa 2024, Kasar Thailand ta kasance ta biyu da ke a kan gaba a fadin duniya wajen safarar Shinkafar da ta kai tan miliyan 8.2.

Wani kwararre a fannin samar da ingantaccen abinci, mai suna James Marsh ya sanar da cewa, wannan Shinkafa wadda ta shafe shekaru goma a ajiye a cikin rumbunan Thailand, sakamakon dadewar da ta yi babu wani sinadari mai gina jikin Dan’adam da za a mora daga cikinta.

A cewarsa, saboda yawan feshen da aka yi mata don kare ta daga lalacewa, zai iya shafar kiwon lafiyar duk wanda ya yi amfani da ita.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa, a ka’ida ba a son buhunhunan Shinkafar da aka adana cikin rumbu su wuce tsawon shekaru biyar a ajiye.

Sannan, ya nuna takaicinsa kan cewa; wadannan buhunhunan Shinkafar, za su samu hanyar shigowa cikin kasar nan duba da yanayin da iyakokin Nijeriya suka kasance.

Ya kuma shawarci gwamnatin tarayya cikin gaggawa ta dauki matakan da suka dace, domin dakile shigo da wannan Shinkafa cikin wannan kasa, inda ya kara da cewa; wannan babban aiki ne a gaban hukumominmu.
Har ila yau, ya sanar da cewa; wannan Shinkafa na dauke da lamba wadda za a iya saurin gane ta.

Shi ma wani kwarrre a fannin kimiyyar abinci da ke Jami’ar Aikin Noma ta Tarayya, Farfesa Shittu Akinyemi ya sanar da cewa, kula da ingancin abinci ya kasu kashi biyu ne, wato yadda aka lula da shi da kuma irin magungunan feshin da aka zuba wa hatsin don kare shi daga kwari.

A cewarsa, ana iya adana hatsi har zuwa dogon zango, sai dai; mutane na jin tsoro kan yadda aka ajiye kayan abinci har zuwa tsawon lokaci, musamman ma Shinkafa.

Shinkafa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Sarki Biyu A Gari Ɗaya: Aminu Ado Ya Isa Kano

Sarki Biyu A Gari Ɗaya: Aminu Ado Ya Isa Kano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.