• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai, Masarautu
0
Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata zanga-zanga ta ɓarke a Kano yau Lahadi da nufin nuna rashin goyon baya da tsige Sarkin Kano Aminu Ado Bayero, inda masu zanga-zangar suke neman a maido da shi kan karagar mulki.

Zanga-zangar wacce aka fara da misalin karfe 4:00pm na yamma bayan kammala addu’a a gidan Sarki da ke Nasarawa, cikin lokaci ƙanƙani ta ƙara faɗaɗa inda masu zanga-zangar suka buƙaci gwamnati da ta bi umarnin kotu tare da maido da Sarki Aminu bakin aiki.

  • Matsayar Ƙungiyar Sarakunan Arewa A Tsaya Kan Umarnin Kotu Kan Rikicin Sarki 2 A Kano
  • An Shawarci Sarki Aminu Ado Ya Fice Daga Kano

Abin mamaki shi ne akwai tarin jami’an tsaro a wurin amma ko kaɗan ba su yi wani yunƙurin hanawa ko taka musu burki ba duk kuwa da cewa suna kallo suke cinnawa tayoyi wuta tare da fasa allunan talla, lamarin da ya baiwa masu zanga-zangar damar cin karensu ba babbaka.Aminu Ado

Masu zanga-zangar waɗanda galibinsu matasa ne, sun yi ta rera waƙoƙin Sarki Aminu Ado tare da ɗaga kwalaye masu ɗauke da saƙonni irin su Abba Kabir Yusuf, Bi umarnin Kotu da “Aminu Har Yanzu Sarkin Mu Ne”. Ɗaya daga cikin masu zanga-zangar Usaini Rabiu Kunya, ya jaddada yadda zanga-zangar tasu ta kasance cikin lumana, ya kuma buƙaci gwamnati da ta bi umarnin shari’a.

Wani mai zanga-zangar, Abubakar Garba, ya roƙi shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya tabbatar da adalci a rikicin masarautar.

Labarai Masu Nasaba

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

Aminu Ado

Zanga-zangar dai ita ce ta baya-bayan nan a rikicin da ya fara kunno kai jihar Kano bayan da majalisar dokokin jihar ta soke dokar da tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje ya yi amfani da ita wajen tsige Sarki Mohammad Sanusi II tare da ƙirƙiro ƙarin sabbin masarautu guda hudu.

Akwai yiwuwar samun ƙarin zanga-zanga a jihar Kano daga dukkan ɓangarorin biyu matuƙar jami’an tsaro ba su ta shi tsaye kan lamarin ba, wani abu da zai ƙara tasiri wajen dagula lissafi shi ne goyon bayan wani sashi daga jami’an tsaro.

Aminu Ado


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BayerokanoMasarautaSunusi Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Majar Jam’iyyun Adawa Na Iya Kawo Karshen Mulkin APC A 2027?

Next Post

Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara

Related

Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago
Manyan Labarai

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

2 hours ago
Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

4 hours ago
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya
Manyan Labarai

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

13 hours ago
Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
Manyan Labarai

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

1 day ago
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
Manyan Labarai

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

2 days ago
Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

2 days ago
Next Post
Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara

Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

June 23, 2025
CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

June 23, 2025
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

June 23, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

June 23, 2025
Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

June 23, 2025
Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

June 23, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

June 23, 2025
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.