• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Da Yaran Nijeriya Ke Ciki

by Leadership Hausa
12 months ago
in Ra'ayoyi
0
yara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ‘Yan Nijeriya suka yi bikin ranar yara na shekara-shekara a farkon wannan makon, babu wani abu na a zo a gani da za a yi farin ciki game da bikin, bisa la’akari da mummunan halin da kasar ke fuskanta wanda yake dakushe fatan rayuwar yaran kasar ta gaba.

Gaskiyar abin da ke da ban mamaki shi ne, irin barazanar da ke neman lalata makomar rayuwar daukacin yara manyan gobe – tun daga sace-sacen da ‘yan ta’adda ke musu da yawaitar rufe makarantu zuwa ga yawaitar ayyukan karfi da ake sa yara da kuma aurar da kananan da ba su kai munzalin aure ba.
Maimakon kare hakki da walwalar yara da kuma ‘yan kasa masu karamin karfi, Nijeriya ta kasance a cikin rikicin da ke kawo cikas ga makomar kasar ita kanta.

  • Ranar Yara Ta Duniya: Inganta Rayuwar Yaran Nijeriya Shi Ne Abu Mafi Girma – Tinubu
  • ‘Yancin Kananan Hukumomi: Kotun Koli Ta Bai Wa Jihohi 36 Kwana 7 Su Kare Kansu

Akwai kididdiga mai sanyaya gwiwa game da ukubobin da suka dabaibaye yaran Nijeriya. Yara miliyan 18.3 ba sa zuwa makaranta, fiye da yawan daukacin al’ummar wasu kasashe.

Idan aka kwatanta da yawan wasu kasashen yadda ya kamata, adadin yaran da ba su zuwa makaranta a Nijeriya ya zarce yawan mutanen kasashen Norway, Singapore, da Cuba. Wannan abin kunya ne kuma bai kamata a bar shi ya ci gaba ba.

A ra’ayin wannan jaridar, wannan mummunar shaida aka yi mana na kasancewa kasa mafi yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a duniya kuma wani tabo ne ga al’ummarmu.

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

A yankunan da ake fama da rikici musamman a arewa maso gabas da arewa maso yamma, neman ilimi ya zama jarumtaka mai hatsarin gaske, inda aka sace ko kuma aka yi garkuwa da yara sama da 1,600 a makarantunsu tun daga shekarar 2014, a cewar kungiyar da ke fafutukar kare lafiyar yara (Sabe the Children.

A cikin watanni uku na farkon shekarar 2024, sama da yara 200 ne ‘yan bindiga suka sace tare da yin garkuwa da su daga ajujuwansu a jihohin Kaduna da Sakkwakoto kadai.
Kamar yadda Daraktan UNICEF na Nijeriya Dr. Tushar Rane ya koka, an rufe makarantu 439 a duk fadin kasar a cikin 2023 saboda ko dai gwamnatoci sun karbe su suna amfani da su ko kuma tsoron kai musu hari.

A yankunan da ke fama da kashe-kashen na Boko Haram da kungiyoyin masu aikata laifuka, ana tilasta wa iyaye “zabi” mai wuya na ko dai su jefa rayuwar ‘ya’yansu cikin hadari don samun ilimi ko kuma su bar su kara-zube cikin rayuwar jahilci da kuma karancin damar zama wani abu a rayuwa.
Wannan matsalar, ba za a iya jure wa zama a cikinta ba, domin tamkar wani mummunan rashin adalci ne da ke take hakkin yaran Nijeriya.

Bugu da kari, duk da haka fa, hare-haren da ake yi a kan makomar rayuwar yaran ba su kare a nan ba. Nijeriya ce kasa ta uku a yawan matan aure a duniya, inda aka aurar da mata miliyan 23.6 kafin su kai ga cika shekara 18 sannan sama da miliyan 10 kafin su kai shekaru 15, a cewar Asusun UNICEF.

An hana su samun ilimi tun a lokacin yarintarsu, wadannan ‘yan matan da ke cikin ukubar rayuwa sun zama kamar wadanda aka yanke musu hukuncin daurin rai da rai, ga rashin lafiya, da kuma bakin talauci da sauran wasu abubuwa da suke fuskanta da ba za a iya kwatantawa ba.

Kamar dai hakan ma bai isa ba, sama da yaran Nijeriya miliyan 24 ne ke gudanar da aikatau (ayyukan karfi da suka sha karfinsu) a shekarar 2022, inda miliyan 14.3 ke gudanar da ayyuka masu hadari, a cewar hukumar kididdiga ta kasa.

Yawancin wadannan yara masu kananan shekaru suna aiki a wuraren ma’adinai masu hadari da masana’antu, ana amfani da su a matsayin tushen arha saboda kudi kalilan ake biyansu, ba kamar manya ba, inda hakan yake hana su samun ilimi, nishadi da walwala da sauran muhimman abubuwan da za su sanya su a cikin farin ciki da ke tattare da yarintarsu.

Wadannan ba kididdiga ba ne kawai ko shata lambobi, manuniya ce ga matsalolin da suka yi wa yara katutu wanda matukar ba a yi wa guru hanci ba, akwai matsala da kuma cikas ga makomar Nijeriya a matsayinta na kasa.

Yayin da miliyoyin mutanen kasar nan ke fuskantar tauye hakkinsu na samun rayuwa mai inganci, rashin makaranta, auren dole, da ayyuka masu hadari, ta yaya kasar za ta iya samar da ‘yan kasa masu ilimi, masu karfin gwiwa da ake bukata don bunkasa tattalin arziki, mulkin dimokaradiyya da ci gaban zamantakewa?
Al’ummar da ta kasa zuba hannun jari a cikin matasanta, tabbas tana asarar dimbin damarta ta habaka jarin Dan‘adam.

Yayin da aka samu ci gaba mai kyau – kamar samun jihohi 34 daga cikin 36 na Nijeriya da suka amince da dokar kare hakkin yara don yaki da cin zarafinsu – amma kuma babu wani katabus wajen aiwatar da dokar domin kare yaran daga fitinar da ke bazaranar tagayyara rayuwarsu.

A bayyane yake, a ra’ayinmu, ana bukatar kwararan matakai da kuma sadaukarwa daga mahukuntan kasa wajen ba da fifiko ga ‘yancin yara, tsaro da walwala.

Dole ne gwamnatin tarayya ta tabbatar da tsaro a cibiyoyin ilimi ta yadda za su zamo yankuna masu aminci, da kara yawan jami’an tsaro da kuma bin diddigin jami’an da ba su tabuka wani abin a zo a gani a kan kula da makarantu.

A yi kokarin hadin gwiwa tare da mara bayan kasafin kudi mai ma’ana domin habaka kai yara makarantu, kawar da aikatau na yara, kawo karshen aurar da yara, da kuma magance tushen matsalolin al’umma da tattalin arziki wadanda suke jefa yaran Nijeriya cikin hadari.

Nuna gazawa kawai ba abu ne da ya dace ba – domin idan har wannan al’ummar ba za ta iya kare kyakkyawan fatan da take da shi ba, da kula da makoma da muhimman hakkoin ‘ya’yanta a yau ba, to za ta illata kanta a gobe, ta kuma kara fadawa cikin talauci da rashin zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Haka nan ya zama wajibi ‘Yan Nijeriya su sanya ido sosai kan kalubalen da ke fuskantar yara da matasan kasar nan.

Ta hanyar kare ‘ya’yanta a yau, Nijeriya za ta kare dimokuradiyyar da ta zaba a matsayin turbar ci gaba da kuma damar da za ta samu na ci gaba a Afirka da duniya. Amma ba da fifikon da ya dace ga gina rayuwar yara shi ne babban sinadarin cimma wannan nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Almajircikarancin Malamaita'ammuli da miyagun kwayoyi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (4): Manzon Allah (SAW) Bai Taba Barin Azumtar Kwanakin Ba

Next Post

Meresca Ya Zama Sabon Kocin Chelsea, Ya Rattaba Hannu A Kwantiragin Shekara 5

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

2 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

6 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

7 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

7 months ago
Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

7 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

8 months ago
Next Post
Meresca Ya Zama Sabon Kocin Chelsea, Ya Rattaba Hannu A Kwantiragin Shekara 5

Meresca Ya Zama Sabon Kocin Chelsea, Ya Rattaba Hannu A Kwantiragin Shekara 5

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.