• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ASUU Ta Bada Wa’adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
ASUU

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta bayar da wa’adin makonni uku ga Gwamnatin Tarayya, inda ta bukaci a warware matsalolin da suka daɗe suna fama da su domin kaucewa yajin aikin da ake shirin shiga.

Shugaban ƙungiyar ASUU reshen Jami’ar Dutse (FUD) jihar Jigawa, Kwamared Salim Ahmed ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron manema labarai na gaggawa.

  • Ranar Nakasassu: Gwamna Uba Sani Ya Nanata Kudirin Shigar Da Su Harkokin Jihar Kaduna
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Kare Haƙƙoƙin Naƙasassu

Ahmed ya soki gwamnatin shugaba ƙasa Bola Tinubu, saboda yin watsi da yunƙurin ƙungiyar na shiga tattaunawa. Batutuwan da ba a warware ba sun haɗa da sake tattaunawa kan yarjejeniyar FGN/ASUU na 2009, jin dadin mambobin ƙungiyar, da cin gashin kan jami’o’i, da samar da kuɗaɗe, da kuma rusa majalisar gudanarwa ba tare da izini ba.

Ƙungiyar ASUU ta kuma bayyana rashin aiki da tsarin Integrated Payroll and Personnel Information System (IPPIS) da kuma rashin biyan kuɗaɗen alawus na Ilimi (EAA).

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta ASUU ta shirya zaburar da mambobinta da wayar da kan al’umma cikin makonni uku masu zuwa. Ahmed ya buƙaci masu ruwa da tsaki da su matsa wa gwamnati lamba domin ta gana da ƙungiyar domin hana afkuwar rikicin da za a iya kaucewa a cikin tsarin jami’o’in.

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ƙungiyar ta jaddada cewa, rashin magance waɗannan matsalolin na iya haifar da ɗaukar matakai na yakin aiki, tare da ƙara kawo cikas ga ɓangaren ilimi da ke da rauni na Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
Nijeriya Ta Koma Matsayi Na 38 A Cikin Sabon Jadawalin FIFA

Nijeriya Ta Koma Matsayi Na 38 A Cikin Sabon Jadawalin FIFA

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
ASUU

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.