• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Dama Ce Ta Bunkasar Duniya

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasar Sin Dama Ce Ta Bunkasar Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumomin kasa da kasa na ci gaba da bayyana kyakkyawan fatansu ga karkon da tattalin arzikin kasar Sin ke da shi, tare da bayyana hasashen ci gaban hakan a shekaru dake tare, suna masu bayyana imanin su ga manyan nasarorin da Sin din ke samu ta fuskar fadadar cinikayya, da kere-keren masanaantu, da daidaito a alkaluman raya tattalin arziki. Ko shakka babu, hakan na kara sanyawa sassan kasa da kasa kara jin karfin gwiwa game da tattalin arzikin Sin.

A tsawon shekaru, kasar Sin na ta daukar matakan dunkulewa, da kara kaimin farfado da tattalin arziki, da samar da sabbin damammaki ga kasashen duniya, musamman masu tasowa ta fuskar ingiza bunkasuwa tare, karkashin shirye-shirye daban daban, irin su dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka ko FOCAC, da shawarar “ziri daya da hanya daya” da sauran su, ta yadda za a kai ga samar da duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil adama.

  • Rikicin Ƴan daba Yayi Sanadin mutuwar mutum 1, Da Raunata 2 A Kano
  • ASUU Ta Bada Wa’adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki

Hukumomi da cibiyoyin hada-hadar kudade na duniya, irin su bankin samar da ci gaba na Asiya, da Goldman Sachs, da Morgan Stanley da sauran su, duk sun daga mizanin hasashen da suka yi na ci gaban tattalin arzikin Sin a shekarar nan ta 2024. Hakan kuma manuniya ce ga yadda Sin din ta zamo muhimmiyar mai samar da daidaito, da ingiza bunkasar tattalin arzikin duniya.

A zahiri take cewa Sin ta taka muhimmiyar rawa, wajen samar da hajoji bisa kyakkyawan farashi ga kasuwannin duniya a matsayinta na babbar cibiyar masanaantu. Tana kuma fadada shigo da hajojin sauran kasashe zuwa babbar kasuwarta mai dinbin jamaa. Kaza lika, matakin Sin na kara bude kofa, da gudanar da sauye-sauye masu inganci, sun kara fadada cudanyarta, da cin gajiya tare da sauran sassan kasa da kasa.

Yayin da Sin ke kara bude kofa ga waje, a daya bangaren tana kara zamanantar da kanta karkashin manufofin samar da ci gaba mai nagarta, inda masharhanta da dama ke ganin babbar kasuwar kasar mai yawan alumma da ta kai sama da biliyan 1.4, za ta ci gaba da bude sabbin babuka na ci gaba da kara farfadowa.

Labarai Masu Nasaba

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Duniya na kara shaida yadda kasar Sin ke ci gaba da raba damammakinta tare da sauran kasashe, ta yadda za a kai ga samun ci gaba mai dorewa, da nasarar dukkanin manufofin gina alummar duniya mai cin gajiyar hadin gwiwar bai daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bunkasar SinJapanKasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Bai Wa ‘Yansanda Umarnin Fitar Da Aminu Ado Daga Fadar Nassarawa 

Next Post

Ya Kamata A Karfafa Manufar Amfani Da Harsunan Gado A Makarantu

Related

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

15 hours ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

16 hours ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

17 hours ago
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
Daga Birnin Sin

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

18 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

1 day ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

2 days ago
Next Post
Ya Kamata A Karfafa Manufar Amfani Da Harsunan Gado A Makarantu

Ya Kamata A Karfafa Manufar Amfani Da Harsunan Gado A Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.