ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Karfafa Manufar Amfani Da Harsunan Gado A Makarantu

by Sadiq
2 years ago
harsunan

Shekaru biyu bayan gwamnatin tarayya ta bayyana manufar harshen da ya kamata a rika koyarwa da shi a makarantu, ba a samu wani ci gaban a zo a gani ba wajen aiwatar da shirin. Makarantu da yawa har yanzu suna amfani da Ingilishi a matsayin harshen koyarwa, kuma an ci gaba da koyar da harsunanmu na gado a matsayin darussa na daban. A wasu makarantun ma,ba su dauki koyar da harsunanmu na gado da muhimmanci ba.

Majalisar zartaswa ta tarayya ta amince da manufar Harsuna ta Kasa (NLP) a shekarar 2022, wanda ya sa harsunan gado suka zama tilas a rika amfani da su wajen koyarwa tun daga aji daya zuwa aji shida na makarantar Firamare.

  • Nijeriya Ta Koma Matsayi Na 38 A Kasashen Da Suka Fi Iya Taka Leda A Duniya
  • Sin Na Goyon Bayan Kokarin Kasashen Afrika Na Magance Matsaloli Ta Hanyar Da Suka Zaba

Shekaru biyar kafin amincewar majalisar zartarwar, a shekarar 2017, gwamnatin tarayya ta bayyana wani shiri na makarantun Firamare da Sakandare na Nijeriya da za a rika koyar da darussan lissafi da kimiyya a cikin harsunan asali. Daga nan sai gwamnati ta kafa kwamitin ma’aikatu da suka hada da ma’aikatar kimiyya da fasaha ta tarayya da ma’aikatar ilimi ta tarayya da za su tabbatar da nasarar shirin.

ADVERTISEMENT

Ana sa ran kwamitin ya samar da wani shiri na bunkasa amfani da harsunan gida da samar da ingantattun kayan aiki don koyar da ilimin lissafi da darussan kimiyya da kyau. Hanya ce da kasashe irin su Sin da Indiya suka dauki shekaru da dama suna amfani da ita a baya, lokacin da suka rungumi dabarun da suka dace da kasashensu da yanayin al’ummominsu ta hanyar koyar da ilmin lissafi da darussan kimiyya a cikin harsunansu na asali a matakin firamare.

Duk da cewa gwamnatin tarayya ta jaddada cewa za a iya aiwatar da manufofin gaba daya ne kawai idan aka samar da kayan koyarwa da kuma samar da kwararrun malamai, amma da alama ba a yi wani abu na cimma hakan ba bayan shekara biyu.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

A kwanan nan, Cibiyar Bunkasa Ci gaban Harshe (LDC) ta ce an fara aiwatarwa amma har yanzu abin yana kan matakin farko. Bayanai sun nuna cewa gwamnati tana kokarin magance kalubalen da ke zama karfen kafa ga shirin kafin manufar ta fara aiki a fadin kasa baki daya. Amma kuma, duk da haka, ba a gani a kasa ba. Kenan a ina gizo yake sakar?

Daya daga cikin manyan dalilan da ke haifar da tafiyar hawainiya a wannan ci gaba na shi ne rashin horar da malamai wadanda za su iya koyar da harsunan gado yadda ya kamata. Dole ne gwamnati ta zuba jari mai yawa a cikin shirye-shiryen horar da malamai don tabbatar da cewa malamai sun sami kwarewar da ta dace don koyar da wadannan harsuna.

Wani kalubale kuma ga samun nasarar shirin shi ne rashin daidaitattun kayan koyarwa a cikin harsunan gado. A ra’ayinmu, dole ne gwamnati ta yi aiki tare da masu buga littattafai don habaka littattafan karatu da sauran kayan aiki na kayan koyarwa a cikin wadannan harsuna. Wannan ba wai kawai zai taimaka wa dalibai su koyi karatu da kyau ba ne, amma kuma zai taimaka wajen adanawa da habaka wadannan harsuna.

Bugu da kari, ya dace a ce manufar ta kunshi litattafai a cikin wadannan harsuna, wadanda za a samar da su domin koyar da ilmin lissafi da kimiyya da horar da malaman da a yanzu za su yi amfani da harsunan wajen koyar da yara a makarantun firamare da sakandare.

A ra’ayinmu, ya kamata gwamnati ta horar da kuma daukar malaman da suka kware wajen amfani da harsunan gida aikin koyarwa a makarantu. Hakan zai tabbatar da cewa ana koyar da dalibai a cikin yarensu na asali kuma za su iya fahimtar darussan da ake koyar da su sosai.

Manufofin harshe da tsarin ilimin ya dauka, babu shakka yana daya daga cikin mafi karfi a cikin salo daban-daban da ake amfani da su wajen sarrafa harshe. Bayan cibiyoyin addini, makaranta ita ce mafi kusa da tsarin amfani da harshen gida. A hakika, yawancin yara suna samun gibi mai yawa a tsakanin yarensu na asali (wanda aka fi sani da yare ko harshen gado) da kuma yaren da ake amfani da shi a makaranta, wanda galibi ana amfani da shi ne a matsayin harshen kasa ko kuma na hukuma.

Amfani da harsunan asali a makarantu yana da fa’idodi da yawa. Yana bai wa dalibai damar koyo cikin harshensu na asali, inganta aiki da ilimin da aka koya da kuma haifar da mafi kyawun sakamako da riko da abin da aka koya. Har ila yau, yana taimakawa wajen adanawa da habaka wadannan harsuna, wanda yake zama wani muhimmin sashi na al’adun Nijeriya. Ana kuma sa ran manufar za ta inganta da kuma kiyaye harsunan Nijeriya.

Haka kuma, koyar da darussan kimiyya da zamantakewa a cikin harsunan asali na iya taimakawa wajen cike gibin da ke tsakanin ilimin da aka gada iyaye da kakanni da kimiyyar zamani. Harsuna na asali galibi suna da kalmomi da ra’ayoyin da babu su cikin Ingilishi,kuma koyarwa a cikin wadannan harsunan na iya taimakawa wajen habaka wannan ilimin a cikin manhajar karatuttuka.

Ya kamata gwamnati ta sanya ido tare da tantance yadda ake aiwatar da manufofin harshe don tabbatar da yin tasiri tare da cimma nasarar da abubuwan da ta kunsa.

+.3Wannan zai taimaka wajen gano wuraren da za a inganta da yin gyare-gyaren da suka dace da manufofin.

Wannan yana nufin cewa domin manufar ta samu nasara, dole ne gwamnati ta zuba jari mai yawa don horar da malamai tare da samar da daidaitattun kayan koyarwa a cikin wadannan harsuna.Ta yin haka, Nijeriya za ta iya taimakawa wajen adanawa da habaka al’adunta tare da inganta ingancin ilimin dalibanta.

A gaskiya, a ra’ayin wannan jaridar, ya kamata gwamnati ta samar da cikakken tsarin manufofin harshe wadanda ke bayyana makasudi, dabaru, da ka’idoji da za a yi amfani da su wajen aiwatar da amfani da harsunan gida a matsayin harshen koyarwa a makarantu.

MASU ALAKA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
Next Post
Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
harsunan

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
harsunan

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.