• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyu Da Suka Fi Daukar Hankali A Hajjin Bana

byBello Hamza
1 year ago
Hajjin Bana

A duk shekara, hukumomin kasar Saudiya na bullo da sabbin tsare-tsare don inganta jin dadin Alhazai da kuma yadda ake gudanar da aikin hajjin.

A shekarun baya an fuskanci rushe -rushe domin fadada wurare ibada masu tsarki inda Alhazai musamman ke yin cincirindo domin gudanar da ayyukan ibada.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • A Guji Ajiye Abinci A Firji Fiye Da Kwana 3 – NAFDAC

Rashin issashen wuri ya haifar da mastaloli da dama a shekarun baya inda har aka kai ga rasa rayukan mutane da dama.

A wannan shekarar Hukumar Saudi ta bullo da katin tantance mai cikakken izinin kasancewa a wurare masu tsari da ake gudanar da aikin hajji. Katin da aka lakaba wa suna NUSUK ya zama wa wasu mahajjata alakakai, musamman ganin an samu jinkiri daga hukumar Alhazai na ba wasu Alhazai wannan katin, musamman lokacin da aka shigo garin Makkah.

Jami’an tsaron Saudiya sun yi ta kama wadanda ke zirga-zirga ba tare da makale da katin NUSUK a wuyarsu ba. Shiga masallacin harami ya gagari Alhazan da basu da katin NUSUK.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Wannan ya sa hukumar Alhazai ta NAHCON ta kara kaimi wajen ganin ta ba kowa katinsa na NUSUK a kan lokaci.

A bayaninsa na cikakken dalilin bullo da katin NUSUK, wani jami’n tsaro na kasar Saudiya wanda ya nemi mu sakaya sunansa saboda bashi da ikon yin magana da ‘yan jarida, ya ce, a shekarun baya bata gari na shigowa cikin tawagar Alhazai inda suke sace-sace musamman a yayin zaman Muna, Arafat da Muzdalifah, sannan kuma hakan zai taimaka wajen takaita hankoron wadanda basu da izinin gudanar da aikin Hajji shiga wurare masu tsarki inda haka yakan haifar da cunkoso, ga duk wanda ya samu gudanar da aikin hajjin bana zai bayyana maka yadda katin NUSUK ta nastar da shi.

Wannan tsari na NUSUK ya taimaka wajen samun cikakken adadin wadanda suka shigo Saudiya domin aikin hajji da kuma kididdigar daga inda suka shigo. Ma’aikatar aikin Hajji da Umara ta ce, alhazai 1,833,164 suka gudanar da aikin hajjin bana daga sassan duniya sun kuma shigo ne ta hanyoyi daban daban.

Wani abu kuma da ya dauki hankalin duniya gaba daya game da aikin hajjin bana, shi ne irin tsananin zafin ranar da aka yi a ranakun jifar jamra, wanda sai ta kai da hukumar kasar Saudiya, a ta bakin Ministan Umara Hajji Abdulfattah bin Suka bayar da umarnin a dakatar da tafiya jamrat na tsawon awa 5, aka kuma umarci Alhazai su lizimci sha ruwa a kai-kai su kuma guji gararamba a cikin ranar ba tare da wani dalili ba.

Hukumomi su da tabbatar da mutuwar mutum 20 yawancin su daga kasashe yankin nahiyar Asiya.

Duk an kammala aikin Hajjn 2024 hasashe ya nuna cewa, za a ci gaba da fuskantar karin zafin rana inda ake ganin zai iya kaiwa 50 zuwa 60 a ma’aunin zafi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Next Post
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA

Rikicin Sarautar Kano: Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnatin Tarayya, APC Ta Mayar Da Martani

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version